Alƙalin Alƙalai, Tanko Muhammad ya yi murabus

Daga BASHIR ISAH

Alƙalin Alƙalan Nijeriya, Mai Shari’a Tanko Muhammad, ya yi murabus daga aiki.

Majiyar tashar Channels Television ta ce Jastis Muhammad ya yi murabus ne a Lahadin da ta gabata saboda dalili na rashin lafiya.

Bayanai sun nuna cewa, an yi nisa da shirye-shirye don rantsar da Alƙali mafi girman muƙami a Kotun Ƙoli, wato Jatis Olukayode Ariwoola, a matsayin Alƙalin Alƙalan Nijeriya mai riƙon ƙwarya.

Haka nan, bayanan sun ce nan ba daɗewa ba za a sanar da naɗin a hukumance.

Kafin yin murabus, rahotanni sun tabbatar da Jastis Muhammad na fama da rashin lafiya sosai.

Idan dai ba a manta ba, a makon da ya gabata ne alƙalan Kotun Ƙolin su 14, suka rubuta wa Muhammad takardar ƙorafi game da taɓarɓarewar yanayin aiki a kotun.

Inda a cikin wasiƙar, alƙalan suka zargi Muhammad da rashin magance matsalolin da suka dabaibaye musu yanyin aikinsu a kotun, da suka haɗa da rashin motocin aiki, rashin muhali, ƙarancin wutar lantarki da sauransu.