02
Jan
DAGA MUKHTAR YAKUBU A watan Agustan ne Gwamnatin Jihar Kano ta nada fitaccen mawaki Tijjani Hussaini Gandu a matsayin Babban Mataimakin na Musamman ga Gwamnan Kano kan harkar wallafa, mukamin da shi ne na farko da aka tava yi a tsarin tafiyar da Gwamnatin Kano. Wakilinmu ya tattauna da Tijjani Gandu domin jin matsayin ofishin nasa da kuma ayyukan da zai rinka gudanarwa. Don haka sai ku biyo mu ku ji yadda tattaunawar ta kasance. MANHAJA Tijjani Gandu, kana daya daga cikin fitattun mawaka a fagen siyasa a kasar nan kuma ka samu kanka a cikin wadanda aka nada a…
