14
May
Daga RABIU SANUSI a Kano A yanayin damuwa kan cece-kuce da ake yi da kuma iƙirari na ƙin biyan kuɗaɗen alawus-alawus na masu shara, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya ba da umarnin biyan ma’aikatan cikin gaggawa. Wannan na zuwa ne daidai lokacin da Gwamnan ya yi wata ganawa ta musamman da ma'aikatan kwashe sharar da shuwagabanninsu a makon nan a ɗakin taro na Coronation dake fadar gwamnati. Gwamna Abba Yusuf ya umarci ma’aikatar muhalli da kula da tsaftar muhalli (REMASAB) da ta tabbatar da biyan duk wasu kuɗaɗen alawus-alawus na masu shara da suka gada daga gwamnatin da ta gabata.…
