20
Oct
Daga MAHDI M. MUHAMMAD Rundunar ’Yan Sandan Nijeriya, reshen Jihar Kano ta ƙaddamar da tubabbun 'yan daba 50 waɗanda ta ɗauka aikin ɗan sanda a jihar bayan kammala horo na wata biyu. Wata sanarwa daga kakakin rundunar, Abdullahi Kiyawa, ta ce an zaɓo mutanen ne daga ƙananan hukumomin Municipal, da Dala, da Ungoggo, da Gwale, da Fagge, inda aka ɗauki mutum 10 kowaccensu. Da yake jawabi ranar Litinin a birnin Kano, Kwamishinan 'Yan Sanda Mohammed Usaini Gumel ya ce 'yan daba 222 ne suka tuba tare da miƙa makamansu a birnin. Birnin Kano ya fuskanci hauhawar faɗan daba da kuma…
