18
Oct
A ranar Talatar da ta gabata Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ƙaddamar da shirin bada tallafi ga 'yan ƙasa na 'Renewed Hope Conditional Cash Transfer', shirin da ake sa ran magidanta miliyan 15 za su amfana da shi. An ƙaddamar da shirin ne a Fadar Villa da ke Abuja albarkacin Ranar Yaƙi da Talauci ta Duniya ta bana. Yayin ƙaddamar da shirin, Shugaba Tinubu ya miƙa cekin N25,000 ga wasu daga cikin waɗanda za su ci gajiyar shirin: Larai Suleiman, Shuaibu Hassana, Sariki Bala Gamu, Okor Jonah da kuma Hameed Kosemani Isiaka. Wakilin Tinubu a wajen taron kuma Sakataren Gwamnatin…
