Editor

9513 Posts
Juyin Mulkin Nijar: Sai bayan shekara uku za mu miƙa mulki ga farar hula – Tchiani

Juyin Mulkin Nijar: Sai bayan shekara uku za mu miƙa mulki ga farar hula – Tchiani

Daga BASHIR ISAH Jagoran juyin mulki a Jamhuriyar Nijar, Abdourahamane Tchiani, ya bayyana cewa sai bayan shekara uku sojoji za su miƙa mulki ga farar hula a ƙasar. Ya bayyana hakan ne a jawabin kai-tsaye da ya yi wa 'yan ƙasar a talabijin ranar Asabar da daddare. Jawabin nasa na zuwa ne bayan tattaunawar da suka yi da tawagar ECOWAS ƙarƙashin jagorancin tsohon Shugaban Ƙasar Nijeriya, Janar Abdulsalami Abubakar (mai ritaya). Janar Tchiani ya ce a tsakanin wata ɗaya mulkin sojin zai kafa kwamitin da zai samar da sabon kundin tsarin mulkin ƙasar. Ya ƙara da cewa, duk da dai…
Read More
An zaɓi Nasiru Mera a matsayin mataimakin shugaban majalisar malamai na ɗaya

An zaɓi Nasiru Mera a matsayin mataimakin shugaban majalisar malamai na ɗaya

Daga JAMIL GULMA a Kebbi Ƙungiyar Izala da ke da shalkwata a Kaduna reshen Ƙaramar Hukumar Mulki ta Argungu da ke Jihar Kebbi ta zaɓi Malam Nasiru Abubakar Mera a matsayin mataimakin shugaban majalisar malamai na 1. Shugaban majalisar malaman Sheikh Suleman Bawa ya bayyana cewa zaɓen Malam Nasiru Abubakar Mera ya biyo bayan la'akari ne da irin gudummawar da ya ke bayarwa wajen da'awa da kuma sauran hanyoyi wajen yaɗawa da ɗaukaka addinin Musulunci. Sabon mataimakin shugaban majalisar malaman ya jaddada cigaba da bayar da duk gudummawar da ya yi wajen ɗaukaka addinin Musulunci tun kama daga da'awa ya…
Read More
Sanata ya raba taki har da ‘yan adawa a Kebbi

Sanata ya raba taki har da ‘yan adawa a Kebbi

Daga JAMIL GULMA a Kebbi A cikin shirinsa na samar da taki don sauƙaƙa wa manoma raɗaɗin wahalar noma, Sanata Yahaya Abubakar Abdullahi mai wakiltar mazaɓar gundumar Kebbi ta Arewa ya raba takin zamani a mazaɓarsa. Da ya ke jawabi jiya Alhamis a wajen ƙaddamar da rabon takin, Shugaban Jam'iyyar PDP na Jihar Kebbi Alhaji Usman Bello Suru ya bayyana cewa Sanata Yahaya Abubakar Mallamawan Kabi ya umarci a bai wa kowa ba tare da la'akari da bambancin jam'iyya ba saboda wakilcin da ya ke yi ba na al'ummar PDP kaɗai ba ne. Haka zalika yana da tabbacin ba 'ya'yan…
Read More
Gwamna Buni ya rantsar da sabbin kwamishinoninsa

Gwamna Buni ya rantsar da sabbin kwamishinoninsa

Daga MUHAMMAD AL-AMEEN, Damaturu Gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni ya rantsar da sabbin kwamishinoninsa 20 tare da ma'aikatunsu daban-daban, inda ya umurce su da bin ƙa'idar aikin. Bikin rantsarwar ya gudana ne a babban ɗakin taron da ke gidan gwamnatin jihar a Damaturu. Gwamna Buni ya yaba wa Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Yobe tare da Mambobinsa bisa gaggauta tantance sunayen kwamishinonin, ya ce hakan ya nuna kyakkyawar alaƙar aiki tsakanin ɓangaren zartaswa da na majalisa don kawo ci gaban al'ummar jihar Yobe. Haka kuma, Gwamnan ya taya sabbin kwamishinonin murna bisa naɗa su Kwamishinoni kuma mambobin Majalisar Zartarwar jihar.…
Read More
Makamashi: Ɓarayin zaune

Makamashi: Ɓarayin zaune

Tare Da BASHIR MUDI YAKASAI Ƙasahe masu albarkacin man fetur a Afirka da sauran ƙasashe masu tasowa a faɗin duniya suna fuskantar matsalar ɓarayin zaune. Su wane ne ɓarayin zaune a waɗannan ƙasashe har da Nijeriya? Maganar gaskiya babu wata ƙunbiya-ƙunbiya su ne manya-manya kamfanoni da suke karakaina a dazuka da gavar tekuna da kuma duk inda hamada ta ke, wato dai dukkan guraren da ake kyautata zaton akwai man fetur da gas. Suna kiran wannan sana’a da ‘exploration and production’, wato bincike da kuma samarwa. Su binciko akwai man fetur ɗin, kuma yawansa ya kai yawan yawan da zai…
Read More
Yanzu ake ganin irin nasarar jajircewar da NEPU ta yi kan talaka – Farfesa Kamilu Fagge

Yanzu ake ganin irin nasarar jajircewar da NEPU ta yi kan talaka – Farfesa Kamilu Fagge

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano An gudanar da taro karo na bakwai a kan ranar tunawa da kafa Jam'iyyar NEPU shekaru 73 da suka gabata da cibiyar nazarin dimukraɗiyya ta Jami'ar Bayero ta gudanar a gidan Mumbayya a ranar Talata. Da yake gabatar da jawabi a yayin taron, Farfesa Kamilu Sani Fagge ya bayyana cewa siyasar aƙida ce ke biyan buqatun jama'a, duk da jam'iyyar NEPU ba ta kafa gwamnati ba amma ta tsaya ta jajirce da yanzu ake ganin nasarar da ta cimma. Ya ce dagewar da NEPU ta yi ne ta ƙwato wa talaka 'yancinsa, yanzu abubuwan da…
Read More
Waɗanda suka zavi Tinubu har sun fara da-na-sani, inji PDP

Waɗanda suka zavi Tinubu har sun fara da-na-sani, inji PDP

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Jam’iyyar PDP, reshen jihar Ondo, ta ce ‘yan Nijeriya da suka zaɓi Jam’iyyar APC a zaven 2023, tuni suka fara nadamar abin da su ka zaɓa. Wannan bayani ya fito ne daga bakin Shugaban Jam’iyyar PDP na Ondo, Fatai Adams, a wata sanarwa da ya fitar ɗauke da sa hannun sakataren yaɗa labaran jam’iyyar, Kennedy Peretei, a Akure, babban birnin jihar. Adams ya ce zabven Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya jawo wa ‘yan Nijeriya wahalhalu, musamman janye tallafin man fetur, wanda ya jefa al’umma cikin halin wahala. Adams yana maida martani ne kan kalaman…
Read More
Gwamnatin Nasarawa za ta yi wa ‘yan mata rigakafin sankarar mahaifa da ta mama

Gwamnatin Nasarawa za ta yi wa ‘yan mata rigakafin sankarar mahaifa da ta mama

Daga JOHN D WADA a Lafiya Gwamnatin Jihar Nasarawa ta bayyana shirin yi wa ‘yan mata masu shekaru tsakanin shekara 9 zuwa 14 rigakafi domin kare su daga kamuwa da cutar sankarar mahaifa da ta mama. Dokta Mohammed Addis, Babban Sakataren Hukumar Kula da Lafiya a matakin farko ta Jihar Nasarawa, NPHDA, ne ya bayyana hakan a wani taron masu ruwa da tsaki da aka yi ranar Alhamis a Lafiya. Ismaila Oko, Manajan Shirye-Shirye, Cibiyar Kula da Rigakafi na Gaggawa ta Jiha ne ya wakilci shugaban a wajen taron. Dokta Addis ya bayyana cewa jihar Nasarawa na cikin jihohi 16…
Read More
Deco ya zama sabon daraktan wasannin Barcelona

Deco ya zama sabon daraktan wasannin Barcelona

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Tsohon ɗan wasan Barcelona Deco ya zama sabon daraktan wasanni a ƙungiyar Ɗan ƙasar Portugal haifaffen Brazil, mai shekara 45, ya rattaba hannu kan kwantiragin shekara uku a Nou Camp. Deco ya fara komawa Barcelona ne daga Porto a shekara ta 2004 kuma ya lashe gasar La Liga sau biyu a kakar wasanni hudu, da kuma gasar Zakarun Turai a shekarar 2006. Barca ta ce Deco ne zai jagoranci sabuwar aƙidar wasansu kuma zai yi aiki tare da koci Xavi da sauran ma su taimaka masa. Ƙungiyar ta ce, tana shirin yi wa ɓangaren gudarwarta garambawul,…
Read More
Mawaƙiya Stephanie ta yi tsirara a Instagram don zagayowar ranar haihuwarta

Mawaƙiya Stephanie ta yi tsirara a Instagram don zagayowar ranar haihuwarta

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Fitacciyar mawaƙiyar Ƙasar Ghana, Stephanie Benson, ta ciyar da idanun mabiyanta da wani rubutu mai daɗi. 'Yar ƙasar Ghana wadda take rayuwarta a Burtaniya, wacce ta cika shekaru 56 a ranar 17 ga watan Agusta, ta bai wa mabiyanta kallon yadda ta yi niyyar yin zama tare da mijinta a ranar ta ta musamman. A cikin wani launin fure da cakuletin hoto, Stephanie Benson ta shafe ilahirin jikinta da mai tare da shimfiɗa wasu furanni daga kafaɗunta ta kuma saukar da cikinta zuwa yankin jibiyarta. Ta kwanta saman qasa sannan ta watsa wasu cakuleti…
Read More