Editor

9513 Posts
Ya yi wuri a yanke ƙauna da Tinubu – Idris

Ya yi wuri a yanke ƙauna da Tinubu – Idris

*Shugaban yana aiki dare da rana don gyara Nijeriya, inji ministan labarai Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Ministan Yada Labarai da Wayar da Kan Jama’a, Alhaji Mohammed Idris, ya roki ‘yan Nijeriya da su kara hakuri da Gwamnatin Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, yana mai cewa, ya yi wuri a yanke kauna ko a dawo daga raikiyar gwamnatin daga lokacin da ya dare gadon mulki zuwa yanzu. Tun da ya hau kan karagar mulki a watan Mayu, Shugaba Tinubu ya bullo da wasu tsauraran sauye-sauye a fannin tattalin arziki, irin su shakewar Naira da kuma cire tallafin man fetur…
Read More
Ayyukan ‘yan daba sun tilasta wa INEC dakatar da zaɓen cike giɓi a Kano da sauransu

Ayyukan ‘yan daba sun tilasta wa INEC dakatar da zaɓen cike giɓi a Kano da sauransu

Daga BASHIR ISAH Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta dakatar da ci gaba da zabe a wasu mazabun da ake sake zabe a jihohin Kano da Enugu da Akwa Ibom saboda matsalolin da suka hada da sace jami'an zabe da sauransu. Yankunan da dakatarwar ta shafa sun hada da Enugu ta Kudu 1, Mazabar Tarsyya ta Ikono/Ini a Akwa Ibom da kuma Mazabar Kunchi/Tsanyawa a jihar Kano. Bayanin haka na kunshe ne cikin sanarwar da INEC dinnta fitar a ranar Asabar mai dauke da sa hannun Kwamishinanta na kasa kan shaa'nin yada labarai, Sam Olumekun. Hukumar ta…
Read More
Gwamna Idris ya yi wa yaran da ba sa zuwa makaranta rajista a Kebbi

Gwamna Idris ya yi wa yaran da ba sa zuwa makaranta rajista a Kebbi

Daga JAMIL GULMA a Birnin Kebbi  Gwamna Nasir Idris ya bayyana cewa gwamnatinsa za ta kira taron ilimi na dukkan masu ruwa da tsaki a fannin ilmi don karfafa dabarun bunqasa ilimi da cigaban ilimi a jihar Kebbi.  Ya bayyana haka ne a wajen bukin kaddamar da rabon kayayyakin ilimi ga yaran da ba su zuwa makaranta a garin Birnin Kebbi a ranar Talatar da ta gabata.  Ya bayyana cewa bayan rantsar da wannan gwamantin kawo yau ta kashe sama da Naira biliyan tara wajen samar da yanayi mai kyau a makarantu da suka hada da gyare-gyare da gina azuzuwa,…
Read More
NAHCON ta bayyana kuɗin Hajjin bana

NAHCON ta bayyana kuɗin Hajjin bana

Daga BASHIR ISAH Hukumar Hajji ta Kasa (NAHCON) ta  bayyana adadin kudin da maniyyata za su biya domin aikin Hajjn 2024. Cikin sanarwar da ta fitar a ranar Asabar ta bakin mai magana da yawunta, Fatima Sanda Usara, NAHCON ta ce game da Hajjin bana maniyyata daga Kudancin Nijeriya za su biya Miliyan N4,899,000, yayin da maniyyata daga Arewacin kasa za su biya Miliyan N4,699,000. Sanarwar ta kara da cewa, maniyyata daga Yola da Maiduguri Naira Miliyan 4,679,000 ne za su biya a matsayin kudin Hajjin 2024. Kafin wannan lokaci, Shugaban NAHCON na Kasa, Malam Jalal Ahmad Arabi, ya yi…
Read More
Cin hanci da rashawa sun ragu a Nijeriya – CISLAC

Cin hanci da rashawa sun ragu a Nijeriya – CISLAC

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Wata kididdiga da Kungiyar Transparency International ta fitar kan rashawa ta nuna cewa an samu ci gaba wajen yaki da matsalar a Nijeriya inda a yanzu jasar ke mataki na 145 cikin kasa 180 da aka yi nazari a kai. Kididdigar ta nuna cewa Nijeriya ta kara maki daya kan maki 24 da take da shi a baya inda a yanzu take da maki 25 cikin 100 baya ga matsawa daga matsayinta na 150. Kididdigar na duba yadda yanayin matsalar rashawa take a gwamnatin kasashen da aka yi nazarinsu. Tana bai wa kowace kasa…
Read More
Hukuncin Kotun Ƙoli: Ban ƙulla wata yarjejeniya da Tinubu ba – Gwamna Abba

Hukuncin Kotun Ƙoli: Ban ƙulla wata yarjejeniya da Tinubu ba – Gwamna Abba

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano a ranar Litinin ya karyata rade-radin dake yi na cewa ya kulla yarjejeniya da Fadar Shugaban Kasa gabanin hukuncin da Kotun Koli ta yanke ranar 12 ga watan Janairu wanda ya tabbatar da zabensa. Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da babban daraktansa na yada labarai da bayanai, Sanusi Bature Dawakin-Tofa, ya fitar a Kano a ranar Litinin. Dawakin-Tofa ya bayyana wata takarda da tuni ta ke yawo tare da nuna wasu yarjejeniyoyi hudu tsakanin gwamna da fadar shugaban kasa a matsayin wata tatsuniyar da…
Read More
Manyan kamfanonin duniya na buƙatar finafinan Kannywood, inji shugaban MOPPAN mai murabus

Manyan kamfanonin duniya na buƙatar finafinan Kannywood, inji shugaban MOPPAN mai murabus

DAGA MUHAMMADU MUJITTABA KANO    "Daga cikin sauye-sauye da Kannywood ta samu a zamani shugabancina shine samun canje canje kasuwancin fina-finai wanda aka dai na cinikin ga wuri ga waina aka koma ta kamfanonin sadarwa na zamani irinsu YouTube, wanda yanzu akwai sama da 500 mai makon da ake saida a CD da makamantansu yanzu an wuce wannan an samu cigaba kuma yanzu akwai manyan kamfanonin duniya irinsu Amazon da suke bukatar finafinan Kannywood, wanda wannan abin farin ciki ne da nasarori da aka samu a zamani na," cewar Dakta Ahmad M. Sarari, Shugaban Hadaddiyar Kungiyar Masu Shirya Finafinai ta…
Read More
Gwamna Nasir ya amince da biyan Naira billiyan 27.5 ga ɗalibai ‘yan asalin Jihar Kebbi 

Gwamna Nasir ya amince da biyan Naira billiyan 27.5 ga ɗalibai ‘yan asalin Jihar Kebbi 

Daga JAMIL GULMA a Birnin Kebbi  Gwamnan jihar Kebbi Dr. Nasir Idris, Kauran Gwandu ya amince da fitar da N27,500,000 domin  gaggauta biyan kudaden daliban da ke karatu a makarantar shari'a a Nijeriya tare da rijistar dukkan 'yan asalin jihar Kebbi 38 dake wannan makarantar.  Wannan yana qunshe ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun kwamishinan shari'a na jihar Dr. Junaidu Bello Marshal wanda ya raba wa manema labarai a Birnin Kebbi a ranar Litinin din da ta gabata.  A cewar kwamishinan, dalibai 28 Bar Part II za su karvi kudi Naira 750,000 (Naira Dubu Dari Bakwai…
Read More
Dattawan Arewa da na Ibo sun tsoma bakinsu kan tafiye-tafiyen Tinubu

Dattawan Arewa da na Ibo sun tsoma bakinsu kan tafiye-tafiyen Tinubu

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Kungiyar Dattawan Arewacin Nijeriya da takwararta ta Ohanaeze Ndigbo mai kare muradun al'ummar Igbo da wasu kungiyoyin farar hula sun bayyana rashin jin dadinsu game da tafiya zuwa Paris da Shugaba Bola Ahmad Tinubu ya yi daidai lokacin da kasar ke fama da karuwar matsalar tsaro. A ranar Laraba 24 ga Janairu ne Shugaba Tinubu ya tafi zuwa Faransa domin wata ziyara ta kashin kai. Wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban, Ajuri Ngelale ya fitar gabanin tafiyar, ta ce Tinubu zai koma Nijeriya cikin makon farko na watan Fabarairu. Sai dai kungiyoyin…
Read More
Sikila: Matar Gwamnan Kebbi ta ƙaddamar da gwaji da bada magani kyauta

Sikila: Matar Gwamnan Kebbi ta ƙaddamar da gwaji da bada magani kyauta

Daga JAMIL GULMA a Birnin Kebbi Matar Gwamnan Jihar Kebbi, Hajiya Nafisa Nasir Idris Shugabar Gidauniyar NANAS Foundation ta kaddamar da gwaji da bayar da magunguna kyauta ga yara masu cutar Sikila guda dari biyu a jihar Kebbi karkashin gidauniyar NANAS Foundation. Wannan tallafin zai zo ne  karkashin hukumar bayar da tallafin kiwon lafiya  Kebbi State Contributory Health Care Management Agency (KECHEMA). Wannan hukumar ce za ta yi musu rajista sannan ta turasu a asibitoci mafi kusa da su domin cigaba da kulawa da su da kuma basu magunguna kyauta.a babban dakin taro na masaukin Shugaban Kasa da ke Birnin…
Read More