02
Feb
Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Hukumar Tsaro ta Sibil Difens, ta cafke wani matashi mai shekaru 24 da a ke zargi da sace mazakutan wasu samari biyar a Karamar Hukumar Dutse ta Jihar Jigawa. Kakakin hukumar, ASC Badrudeen Tijjani Mahmud ne ya sanar da hakan yayin ganawa da manema labarai a ranar Alhamis. A cewarsa, matashin da ake zargi ya fito ne daga kauyen ’Yan Ciyawa na Karamar Hukumar Nguru ta Jihar Yobe. Ya ce a ranar Litinin 29 ga watan Janairu ne suka kama matashin kan zargin sace mazakutan wasu samari biyar a unguwar Gida Dubu da ke…
