Editor

9307 Posts
Ba abin da ya fi a rayuwar mace kamar ɗora ta kan hanyar ilimi – Mariya Durumin Iya

Ba abin da ya fi a rayuwar mace kamar ɗora ta kan hanyar ilimi – Mariya Durumin Iya

"Mace na rayuwa ne ƙarƙashin kulawar wasu har ƙarshen rayuwarta" Ci gaba daga makon jiya Daga AISHA ASAS A satin da ya gabata, mun fara shimfida kan tattaunawar da muke yi da daya daga cikin matan Arewa da suke da gidauniyar taimakon al'umma, inda muka soma da jin tarihin rayuwarta, yadda ta fara tunanin bude wannan gidauniyar da kuma hanyoyin da ta bi har hakarta ta cimma ruwa. A wannan sati, za mu soma ne da samar wa masu karatu amsar tambayar da muka kwana kanta, kamar yadda muka yi alkawari, kafi wasu tambayoyin su biyo baya. Har wa yau…
Read More
‘Yan bindiga sun sako Shugaban Karamar Hukumar Akwanga bayan biyan kuɗin fansa

‘Yan bindiga sun sako Shugaban Karamar Hukumar Akwanga bayan biyan kuɗin fansa

Daga BASHIR ISAH Shugaban Karamar Hukunar  Akwanga a Jihar Nasarawa, Safiyanu Isah Andaha, ya shaƙi iskar 'yanci bayan da 'yan bindiga suka yi garkuwa da shi. An sako shi ne tare da  abokinsa, Adamu Custom da wasu mutum biyu wadanda aka yi garkuwa da su a lokaci guda ranar Litinin da daddare. MANHAJA ta kalato cewa, sai da aka biya fansar Naira miliyan 10 kafin aka sako wadanda lamarin ya shafa. Majiya da ta bukaci a dakaya sunanta ta bayyana cewa, an saki wadanda aka yi garkuwa da su din ne a bayan wani gidan mai da ke hanyar Bayan…
Read More
Gwamnati ta yi watsi da shirin karin kudin wutar lantarki

Gwamnati ta yi watsi da shirin karin kudin wutar lantarki

Daga BASHIR ISAH Gwamnatin Tarayya ta yi tsayin daka kan kin amicewa da karin farashin wutar lantarki kamar yadda kamfanin samar da lantarki na Nijeriya ya bukata. Ministan Makamashi, Adebayo Adelabu, shi ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Litinin. Ministan ya jaddada kudurin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu na tabbatar da wadatacciyar wutar lantarki a kasa. Adelabu ya kara da cewa, “Rashin damarmaki na ci gaba da zama babban kalubalen da fannin lantarki ke fuskanta. “Muna yin nazari kan tsarin aiwatar da jadawalin kuɗin fito tare da tabbatar da ci…
Read More
2023: Shekarar sace ’yan makaranta da tsadar rayuwa

2023: Shekarar sace ’yan makaranta da tsadar rayuwa

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Wannan mako shi ne na karshe cikin wannan shekara ta Miladiyya ta 2023, ga masu nisan kwana. Cikin yardar Allah mai kowa mai komai, mun kasance cikin masu rai da lafiya da suka ga wannan shekara. Da fatan Allah zai ja kwanakinmu mu ga shekara mai zuwa cikin rayayyu. Abubuwa da dama sun faru da za su dade a zukatan ’yan Nijeriya, na dadi da akasin haka, wadanda za a yi ta tunawa da su, saboda tasirinsu a rayuwarmu. Kama daga shirye-shiryen Babban Zaven 2023 da kafa sabuwar gwamnati, cire tallafin man fetur, tsadar rayuwa, hukuncin…
Read More
A yanzu ana kallon marubuci kamar wanda bai san kansa ba – Ayusher Muhammad

A yanzu ana kallon marubuci kamar wanda bai san kansa ba – Ayusher Muhammad

"Kaso sittin bisa ɗari Ina wa rubutu kallon sha’awa ne" DAGA MUKHTAR YAKUBU Aisha Muhammad Salis, wadda aka fi sani da Ayusher Muhammad a harkar rubutun onlayin, ta na daga cikin fitattun marubutan soshiyal midiya da a yanzu ake yayin su. Haka kuma tana da basira da salon kirkirar labari da rubutawa. Don haka ne ma ta yi fice a cikin marubutan da ake ji da su a onlayin. Domin jin ko wacece Ayusher, wakilin Blueprint Manhaja a Kano, ya tattauna da ita, don haka sai ku biyo mu ku ji yadda tattaunawar ta kasance. MANHAJA: Da farko dai za…
Read More
Hannutu Musawa ta buƙaci a tallafa wa jarumi Zack Orji kan jinyarsa

Hannutu Musawa ta buƙaci a tallafa wa jarumi Zack Orji kan jinyarsa

Daga BASHIR ISAH Ministar Kirkire-kire da Al’adu, Barista Hannatu Musawa, ta yi kira ga masu hali a Nijeriya da su dubi Allah su taimaka wa jarumin masa’antar Nollywood, Zack Orji, bisa jinyar da yake yi a halin yanzu. A ranar Litinin da ta gabata aka yi wa jarumin aiki na lalurar da yake fama da ita mai nasaba da kwakwalwa. Wata sanarwa da ta fitar a ranar Laraba mai dauke da sa hannun hadimarta, Nneka Ikem Anibeze, ta ce Hannatu ta yi wannan roko ne bayan da ta ziyarci jarumin a asibitin da yake jinya da ke yankin Wuse a…
Read More
Zargin N17bn: Tinubu ya bada umarnin dakatar da binciken da ake yi wa Halima Shehu

Zargin N17bn: Tinubu ya bada umarnin dakatar da binciken da ake yi wa Halima Shehu

Daga BASHIR ISAH Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, ya bada umarni kan gaggauta dakatar da binciken da ake yi wa Shugabar shirin NSIPA, Halima Shehu. Kazalika, Tinubu ya amince da nadin Dokta Akindele Egbuwalo don maye gurbin Halima a matsayin mukaddashi. Idan za a iya tunawa, ‘yan watanni da suka gabata ne gwamnatin Tinubu ta nada Halima shugabancin NSIPA. Tun farko, rahotanni sun nuna hukumar yaki da rashawa ta EFCC ta tsare Halima a Talatar da ta gabata. An tsare ta ne jim kadan bayan da Shugaba Tinubu ya dakatar da ita daga mukaminta bisa zargin tura kudaden NSIPA Naira…
Read More
Kashi 70 na kudin Gadar Ɗan-agundi

Kashi 70 na kudin Gadar Ɗan-agundi

Daga MUHAMMAD SHAMSUDDEN Na karanta ra'ayoyi mabanbanta a kan wannan maganar, in da mafi yawan masu sharhi suka bayanna rashin gamsuwarsu da wannan tsari. Rubutun da suka fi daukar hankalina a dandalin Fesbuk su ne na Barista Abba Hikima da kuma na Malam Misbahu Baffa Na 'Yar Talla , ba kawai saboda zurfin iliminsu da hangen nesansu ba, a'a, saboda kokarinsu na tsage gaskiya da rashin siyasantar da abin da ya shafi al'umma. Dukkan wadannan kwararrru sun nuna rashin dacewar wannan tsari, duk da dai dan gajeren rubutu suka yi ba tare da cikakken sharhi ba, watakila saboda suna gudun…
Read More
IPPIS: Wasu mutane 6 da suka shaƙe wuyan ilimin jami’o’in gwamnati a Nijeriya

IPPIS: Wasu mutane 6 da suka shaƙe wuyan ilimin jami’o’in gwamnati a Nijeriya

Daga MUHAMMAD SULAIMAN ABDULLAHI Murnata daya, Buhari da ransa yana gani, an yi abin da gwamnatinsa ta sa aka lalata karatun jami'a da shi. Amma watakila cirewar ba wani cikakken amfani za ta yi ba, domin aikin gama dai ya riga ya gama. Yawancin jami'o'inmu a yanzu suna cikin tsananin wahala. Tsarin IPPIS din nan, da a ce an shirya adalci a cikinsa, ta hanyar cikashe wawaka-wawakan gibukan da ya zo da su, da kila ba shi da wata matsala, amma suna kallo mutanen jami'a suka ce zai cutar da mu, amma suka yi kememe, wai su ga masu mulki.…
Read More
Fassarar jawabin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu a sabuwar shekarar 2024

Fassarar jawabin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu a sabuwar shekarar 2024

Ya ku `yan uwana 'yan Nijeriya, ina cike da farin ciki a yayin da nake wa Ilahirinmu, matasa da tsofaffi maraba da shigowa sabuwar shekara ta dubu biyu da ashirin da hudu. Dole ne mu daga hannuwanmu sama mu gode wa Allah Madaukakin Sarki saboda albarkar da Ya yi wa kasarmu da kuma rayukan mu a cikin shekarar da ta gabata wato shekara ta dubu biyu da ashirin da uku. Kodayake shekarar da ta gabata na kunshe da kalubale da dama, amma duk da haka an yi abubuwan alheri masu yawa, ciki har da mika mulki daga tsohuwa zuwa sabuwar…
Read More