30
Jan
Daga BASHIR ISAH A ranar Talata aka rantsar da Hon. Oludaisi Elemide a matsayin sabon Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Ogun inda ya maye gurbin Olakunle Oluomo wanda ska tsige shi a matsayin kakin majalisar makon jiya. Yayin zaman majalisar karkashin jagorancin Mataimakin Shugaban Majalisar, Bolanle Ajayi wanda ya samu halarcin mambobi 22, Hon. Musefiu Lamidi ya karanto rahoton kwamitin da majalisar ta kafa don binke kan zarge-zargen da ake yi wa Oluomo. Rahoton Kwamitin ya ce rashin da'ar da tsohon Kakakin ya nuna wa Kwamitin a lokacin gudanar da bincikensa rashin martabaws ne ga Kwamitin da ma Majalisar baki daya.…
