Editor

9513 Posts
Gwamnan Kano zai yi dokar aiwatar da aikin gwamnati ta fasahar sadarwa

Gwamnan Kano zai yi dokar aiwatar da aikin gwamnati ta fasahar sadarwa

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Gwamnatin jihar Kano na shirin samar da dokar da za ta bada cikakkiyar damar aiwatar da tsarin gudanar da aikin gwamnati ta amfani da fasahar sadarwa a duk fadin jihar, domin saukaka ayyukan gwamnati da bunkasa fannin tattalin arzikin ta amfani da fasahar sadarwa. Gwamna Abba Kabir Yusuf ne ya bayyana haka ne a wajen rufe taron Majalisar Sadarwa, kirkira da fasahar sadarwa karo na 11, wanda ya gudana a dakin taro na Coronation dake gidan gwamnati Kano jiya Alhamis. A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature ya aikowa Manhaja…
Read More
Hatsarin mota ya yi sanadiyar mutuwar ƙawayen amarya shida a Neja

Hatsarin mota ya yi sanadiyar mutuwar ƙawayen amarya shida a Neja

Da yammacin Juma'ar da ta gabata hatsarin mota ya yi sanadiyar mutuwar aƙalla wasu matasa shida a kan hanyarsu ta rakiyar amarya a yankin Ƙaramar Hukumar Edita, Jihar Neja. Shafin Tsalle Daya da ke Facebook ya ruwaito cewa, waɗanda lamarin ya shafa ƙawayen amarya ne su shida da kuma wani ƙanin ango ɗaya. Ya zuwa haɗa wannan labari, babu wani bayani a hukumance game da hatsarin walau daga ɓangaren 'yan sanda ko Hukumar Kiyaye Haɗurra daga yankin.
Read More
Legas ta zarce Dubai da Barcelona wajen samun masu ziyara a duniya

Legas ta zarce Dubai da Barcelona wajen samun masu ziyara a duniya

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Legas ta doke Dubai, Barcelona, Miami inda ta zama birni na 19 mafi kyawun ziyarta a duniya. Rahoton Time Out, wani kamfanin watsa labarai na Birtaniya ne ya bayyana hakan. Time Out ya ce, an yanke wannan shawarar ne daga wani bincike na sama da birane 20,000 a fadin duniya. A cikin rahoton da aka buga a ranar Talata, Time Out ya ce ya yi aiki tare da Potentia Insight, wani kamfanin bincike, don karfafa ingancin binciken. Cape Town na Afirka ta Kudu, Legas na Nijeriya da Accra na Ghana ne kawai biranen Afirka da suka…
Read More
Babu kai babu ƙuri’armu a 2027, gargaɗin Ƙungiyar Dattawan Jihar Katsina ga Tinubu

Babu kai babu ƙuri’armu a 2027, gargaɗin Ƙungiyar Dattawan Jihar Katsina ga Tinubu

Daga UMAR GARBA a Katsina Kungiyar Dattawan Jihar Katsina ta nuna adawarta game da sauya wa wasu hukumomin gwamnati mazauni da Gwamnatin Tarayya ke yi a halin yanzu, ciki har da dauke aikin fadada filin jirgin sama na Malam Umaru Musa 'Yar'adua dake Katsina wanda gwamnatin tsohon Shugaban Kasa, Muhammadu Buhari ta bada kwangilar aikin don inganta shi. Rahotanni sun bayyana cewar Gwamnatin Tarayya karkashin jagorancin Bola Ahmed Tinubu, ta bayyana aniyarta na dauke wasu rassa na Babban Bankin Nijeriya daga Abuja zuwa Jihar Lagos da kuma sauya wa hedikwatar Hukumar Kula da Filayen Jiragen Sama ta Kasa (FAAN) zuwa…
Read More
Rage adadin masu taimataka wa Shugaban Ƙasa zai shafi ayyukan gwamnati – Tinubu

Rage adadin masu taimataka wa Shugaban Ƙasa zai shafi ayyukan gwamnati – Tinubu

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Shugaban Kasa Bola Tinubu, ya bayar da hujjar cewa ministocinsa 47 ne a majalisar ministoci, inda ya ce adadin ya nuna irin ayyukan da ake bukata domin tafiyar da gwamnati mai inganci. Shugaban ya nuna shakku kan rage yawan majalisar ministocinsa, yana mai cewa babu tabbacin hakan zai inganta ayyuka. Ya kuma bukaci shugabannin kungiyar Kiristoci ta Nijeriya da su yada sakon haquri da fata a tsakanin ’yan Nijeriya, yana mai gargadin cewa akasin haka na iya cutar da kasar nan ba tare da gyarawa ba. Tinubu, wanda ya jaddada rawar da shugabannin addinai ke takawa…
Read More
Filato: Hedikwatar Tsaro ta gayyaci shugaban CAN kan zargin sojoji da kisa

Filato: Hedikwatar Tsaro ta gayyaci shugaban CAN kan zargin sojoji da kisa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Hedikwatar Tsaro ta sojoji ta bayyana aniyar ta na ganawa da Rev Timothy Daluk, Shugaban Kungiyar Kiristoci ta Nijeriya a Karamar Hukumar Mangu ta Jihar Filato. Daluk ya zargi sojojin Nijeriya da sa ido kan kashe-kashen Kiristoci da lalata dukiyoyi a jihar. A wani faifan bidiyo da ya fito, Daluk ya yi zargin cewa sojojin Nijeriya na da hannu wajen kashe Kiristoci da varnata dukiya a jihar. Ya yi ikirarin cewa sojoji na da hannu wajen korar Kiristoci tare da barin wasu gungun ’yan bindiga sun kona gidajensu a karamar hukumar Mangu. A halin da ake…
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: Kotun Ƙoli ta tabbatar da hukuncin ɗaurin shekara biyar kan Farouk Lawan

Da Ɗumi-ɗumi: Kotun Ƙoli ta tabbatar da hukuncin ɗaurin shekara biyar kan Farouk Lawan

Daga BASHIR ISAH Kotun Koli ta tabbatar da hukuncin daurin shekara biyar da a baya kotu yanke kan a kan tsohon dan Majalisar Wakilai, Farouk Lawan, bayan da ta kama shi da laifin karbar cin hancin $500,000 daga hannun Femi Otedola. Lawan ya daukaka kara zuwa Kotun Koli ne inda ya nemi kotun ta yi watsi da hukuncin da Kotun Daukaka Kara ta yanke a kansa ran 24 ga Fabrairun 2022 wanda ta daure shi shekara biyar a gidan yari. Sai dai, hukuncin da Mai Shari’a John Okoro ya rubuta wanda Mai Shari’a Tijjani Abubakar karanta, kotun ta yanke cewa…
Read More
Ƙungiyar ’Yan Kasuwar Arewa sun gudanar da babban taro a Nasarawa

Ƙungiyar ’Yan Kasuwar Arewa sun gudanar da babban taro a Nasarawa

Daga JOHN D. WADA a Lafiya A ’yan kwanan nan ne wata hadaddiyar Kungiyar 'Yan Kasuwar Arewacin Kasar nan bakidaya da ake kira 'Northern Traders Association' a Turance wadda ta kunshi duka jihohin arewa na kasar nan 19 ta gudanar da wani gagarumin taron ta a garin Lafiya babban birnin jihar Nasarawa don tattauna wasu matsaloli da kalubale da ke addabar ’ya’yan kungiyar bakidaya. A jawabin sa na maraba Shugaban kungiyar na kasa alhaji Baba Usman Jos wanda mataimakin sa alhaji Jahi Abdullahi ya wakilce shi ya bayyana cewa kungiyar ta ga ya dace ne ta hada babban taron don…
Read More
An dakatar da kocin Union Berlin kan naushin ɗan wasa

An dakatar da kocin Union Berlin kan naushin ɗan wasa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD An dakatar da kocin kulob ɗin Union Berlin Nenad Bjelica wasanni uku saboda naushin dan wasan Bayern Munich Leroy Sane a fuska. Lamarin ya faru ne a minti 74 na wasan da suka buga a Bundesliga a ranar Laraba, lokacin da Sane ke kokarin daukar kwallo a hannun Bjelica yayin da ta fita jifa. Bjelica wanda aka ci tarar yuro 25,000 sau biyu yana sa hannu a fuskar Sane, yana tura shi, amma daga baya an kore shi daga wasan. Ya nuna dabi’ar da ba ta ’yan wasa ba, kamar yadda hukumar kwallon qafa ta Jamus…
Read More
Ganduje ya kai gaisuwar ta’aziyya ga iyalan Sheikh Yusuf Ali

Ganduje ya kai gaisuwar ta’aziyya ga iyalan Sheikh Yusuf Ali

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaban Jam'iyyar APC na Kasa kuma tsohon Gwamnan Jihar Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya kai gaisuwar ta'aziyya ga iyalan Sheikh Iman Dr Yusuf Ali (Sarkin Malaman Gaya) jiya Alhamis. Shugaban jam'iyyar ta APC ya nuna alhininsa bisa rasuwar shehin malamin sannan ya jaddada cewa rashin Shehun ba wai na iya iyalansa ba ne shi kadai, rashi ne nasu su aminansa da kuma al'ummar duniya. "Saboda Sheikh Yusuf Ali ya karar da rayuwarsa ne gabadaya kan yada addinin Musulunci da jan hankali kan koyarwarsa," inji Ganduje. Tawagar ta Shugaban Jam'iyyar ta hada da dukkan…
Read More