28
Jan
Daga MAHDI M. MUHAMMAD Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta bayar da umarnin garkame wasu magoya bayan gwamna Siminalayi Fubara su biyar a gidan gyaran hali na Kuje, Abuja, bisa zarginsu da hannu wajen kona ginin Majalisar Dokokin jihar Ribas da ke Fatakwal, Jihar Ribas. Mai shari’a Bolaji Olajuwon ya ba da umarnin ne a ranar Alhamis, 25 ga watan Janairu, 2024, jim kadan bayan gurfanar da su a gaban kotu kan tuhume-tuhume bakwai da suka shafi ta’addanci da kisan kai. Ko da yake sun qi amsa dukkan tuhume-tuhumen da ake tuhumar su da su, amma alkalin kotun…
