Nishadi

Soke lasisin ‘yan Kannywood: MOPPAN da KSCB sun cimma matsaya

Soke lasisin ‘yan Kannywood: MOPPAN da KSCB sun cimma matsaya

Daga AISHA ASAS Hukumar Tace Finafinai ta Jihar Kano, ƙarƙashin jagorancin Malam Abba El-Mustapha ta janye yunƙurinta na ƙaƙaba wa 'yan fim dokar soke lasisinsu da ta shelanta yi a kwanakin baya. Hukumar ta ce, a yanzu za a sabunta wa masu harkar fim rijistansu ne a ƙarƙashin ƙungiyoyin masu shirya finafinai, waɗanda ke ƙarƙashin Haɗaɗɗiyar Ƙungiyar Masu Shirya Finafinai ta Nijeriya, wato MOPPAN. Wannan sauyin ya biyo bayan ziyarar da ƙungiyar MOPPAN ƙarƙashin jagorancin shugabanta na ƙasa, Dakta Ahmed Sarari ta kai wa shugaban hukumar ta tace finafinai. Bayanin wanda yake ƙunshe a wata takardar sanarwa ga manema labarai…
Read More
Mutane 1,040 ne suka amfana da tallafin kayan abinci da mawaƙi Rarara ya yi a Katsina

Mutane 1,040 ne suka amfana da tallafin kayan abinci da mawaƙi Rarara ya yi a Katsina

Daga AISHA ASAS Shahararren mawaƙin siyasa, kuma babban mawaƙin Jam'iyyar APC, Dauda Kahutu Rarara, ya bayar da tallafin kayan abinci ga mabuƙata, a ƙoƙarin ganin ya bayar da tasa gudunmawa a samun sasaucin matsin rayuwa da ake ciki. Mawaqin ya bayar da wannan tallafi ne a mahaifarsa, Kahutu da ke Ƙaramar Hukumar Danja, ta Jihar Katsina, kamar yadda babban mai taimaka wa mawaqin a kafafen sada zumunta Rabi'u Garba Gaya ya bayyana. Rabi'u ya ce, Rarara ya gudanar da rabon kayan ne a mahaifarsa da ke Kahutu, sannan an bai wa kowanne mutum ɗaya daga cikin mutanen 1,040 ƙaramin buhun…
Read More
Ƙungiyar Mawaƙan Sabon Rai ta Cocin Ikilisiya sun karrama tsofaffin shugabanin ta

Ƙungiyar Mawaƙan Sabon Rai ta Cocin Ikilisiya sun karrama tsofaffin shugabanin ta

Daga RABI'U SANUSI A ranar Lahadi ne ƙungiyar kai bushara ta mawaƙan sabon rai da ke cocin Ikilisiyar Angilican ta Ƙaramar Hukumar Fagge cikin Jihar Kano ta karrama tsofaffin shugabanin ta da sukai aiki tuƙuru da cigaban yaɗa addini Kiristanci. Kamar yadda tsohon ɗan takarar majalisar jiha na Ƙaramar Hukumar Rogo, kuma mai tsawatarwa a wannan ƙungiya, Hon Haruna Yahaya Kadana ya yi ma manema labarai ƙarin haske jim kaɗan bayan kammala taron karramawar bayan gudanar da addu'o'i kamar yadda aka saba a duk ranakun Lahadin mako. Haruna Kadana ya ce, bai taɓa tunanin zai zama ɗaya daga cikin waɗanda…
Read More
Jarumi Kanayo O. Kanayo ya gargaɗi masu fim kan yadda suke yaudara ta hotuna da kwalliya a finafinansu

Jarumi Kanayo O. Kanayo ya gargaɗi masu fim kan yadda suke yaudara ta hotuna da kwalliya a finafinansu

Daga AISHA ASAS Shahararren ɗan wasan fim a masana’antar Kudu, wato Nollywood ya gargaɗi masu shirya finafinai kan yadda suke bayyana ababen da ke voye gaskiyar rayuwa ta mutanenmu, ta hanyar amfani da aiki daban da abinda yake zahiri, tare kuma da kwaikwayon ababen da suka bambanta da ababen da muka sani, wanda hakan ke kai masu kallo ga ruɗani kan wanene daidai, tsakanin gaskiya da kuma abinda ake nunawa, yayin da ta wani vangaren zai iya zama silar rashin tagomashin finafinan, dalilin gyara da mai kallo zai ta cin mai shiryawa. Jarumin ya yi wannan kira ne a ranar…
Read More
Duk mai son kawo ɓarna a Kannywood ya kama gabansa, don yanzu lokacin gyara ne, inji Abba El-Mustapha

Duk mai son kawo ɓarna a Kannywood ya kama gabansa, don yanzu lokacin gyara ne, inji Abba El-Mustapha

Daga IBRAHIM HAMISU, a Kano Sabon Shugaban Hukumar Tace Finafinai da Ɗab'i ta Jihar Kano ya sha alwashin duk mai yiwuwa wajen kawo gyara da kyautata ɗabi'un jama'a a matsayin sa na shugaban hukumar iya tsawon lokacin da Allah ya ba shi dama zai yi a kujerar shugabancin nasa. Abba El-Mustapha ya bayyana hakan ne a ranar Litinin 24 ga Yuli, a lokacin da yake jawabi a gaban ɗumbun jama'a na cikin masana'antar Kannywood da kuma masoyansa da suka raka shi ofishinsa domin kama aiki. Abba El-Mustapha ya fara da cewa, "Ni ɗan fim ne da ke taka rawa da…
Read More
HOTUNA: Gwamna Abba ya miƙa wa Abba El-Mustapa takardar naɗi

HOTUNA: Gwamna Abba ya miƙa wa Abba El-Mustapa takardar naɗi

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya miƙa wa jarumi a masana'antar Kannywood, Abba El-Mustapha, takardar naɗin da ya yi masa kwanan nan. Gwamna Abba ya naɗa El-Mustapha ne a matsayin Babban Sakataren Hukumar Tace Fina-finai ta Jihar. Sakataren Gwamnatin Jihar Kano, Dr Abdullahi Baffa Bichi shi ne ya miƙa wa El-Mustapha takardar a madadin Gwamna Abba. Ga ƙarin hotunan yadda taron miƙa takardar ya kasance:
Read More
Cibiyar Kannywood Foundation ta taya jarumi El-Mustapha murna

Cibiyar Kannywood Foundation ta taya jarumi El-Mustapha murna

Daga WAKILINMU Cibiyar Kannywood Foundation ta yi taya murna ga jarumi Abba El-Mustapha naɗin da Gwamnan Kano ya yi masa kwanan nan. Gwamna Abba Kabira ya naɗa Abba El-Mustapha ne a matsayin Babban Sakataren Hukumar Tace Fina-finai da Ɗab'i ta Jihar Kano, wato KSCB. Cikin sanarwar da ta fitar mai ɗauke da sa hannun jami'in hulɗa da jama'a na cibiyar, M.K Maikaba, cibiyar ta ce "Gaba ɗayanmu shugabani da 'ya'yan wannan cibiya na matuƙar farin cikin samun tabbacin wannan muhimmin labari. "Don haka muke yi wa Allah Mai Girma godiya, sannan muna son mu nuna wa Mai girma zaɓaɓɓen Gwamnan…
Read More
Jarumi Abba El-Mustapha ya zama Shugaban Hukumar Tace Finafinai

Jarumi Abba El-Mustapha ya zama Shugaban Hukumar Tace Finafinai

Daga AISHA ASAS Tun bayan sauya gwamnatin Jihar Kano, ake muhawara kan wanda za a ba wa ragamar shugabantar Hukumar Tace Finafinai ta Jihar Kano, lamarin da ya zama abin tattaunawa a shafukan sada zumunta. Duk da mutane da dama sun faɗi ra'ayinsu kan waɗanda suke hasashen za su iya ɗarewa kujerar shugabancin hukumar, kamar Sunusi Oscar 442, Hamisu Lamiɗo Iyan-Tama, Salisu Muhammad Officer, sai dai da yawa sun aminta da cewa, a dukka mutanen da ake zayyanowa ba wanda ake hasashen zai iya danne fitaccen jarumi Abba El-Mustapha sakamakon irin rawar da ya taka a siyasar Kwankwasiyya da kuma…
Read More
Mawaƙi Ado Gwanja zai angonce yau Juma’a

Mawaƙi Ado Gwanja zai angonce yau Juma’a

Daga AISHA ASAS An kwana biyu ana raɗe-raɗen shahararren mawaƙin mata, Ado Gwanja, zai yi sabon aure bayan rabuwarsa da matarsa ta farko wadda suke da ‘ya ɗaya tilo da ita, sai dai babu wata hujja da ke nuna gaskiyar zancen, wanda hakan ke sa lokacin ya zo ya wuce ba tare da an ji labarin ɗaura auren ba. Sai dai a wannan karon labarin ya bambanta, domin ya samu isnadi mai ƙarfi da za a iya cewa ƙamshin gaskiyarsa ya rinjaye warin ƙaryarsa, domin labarin ya fito ne daga bakin yayan mawaƙin Alhaji Sa’idu Gwanjo, wanda ya sanar da…
Read More
Fitattun mawaƙan Nijeriya da suka taɓa zaman gidan kaso

Fitattun mawaƙan Nijeriya da suka taɓa zaman gidan kaso

(Ci gaba daga makon jiya) Daga AISHA ASAS A satin da ya gabata, mun kawo wasu daga cikin mawaƙan da suka ɗanɗani zaman gidan yari da kuma dalilan da ya kai su. Sannan mun yi ma ku alƙawarin ci gaba da wannan darasi, don samun kawo ƙarin wasu kafin mu rufe darasin. Shahararrun mawaƙa da suka yi rayuwar gidan kaso na ɗan da dama, don haka ba za mu iya kawo wa masu karatu dukka ba, saboda haka za mu tsakuro ne daga ciki. A sha karatu lafiya. Burna Boy: Mawaƙi Burna Boy ba ya buƙatar gabatarwa a wannan zamani…
Read More