08
Aug
Daga AISHA ASAS Hukumar Tace Finafinai ta Jihar Kano, ƙarƙashin jagorancin Malam Abba El-Mustapha ta janye yunƙurinta na ƙaƙaba wa 'yan fim dokar soke lasisinsu da ta shelanta yi a kwanakin baya. Hukumar ta ce, a yanzu za a sabunta wa masu harkar fim rijistansu ne a ƙarƙashin ƙungiyoyin masu shirya finafinai, waɗanda ke ƙarƙashin Haɗaɗɗiyar Ƙungiyar Masu Shirya Finafinai ta Nijeriya, wato MOPPAN. Wannan sauyin ya biyo bayan ziyarar da ƙungiyar MOPPAN ƙarƙashin jagorancin shugabanta na ƙasa, Dakta Ahmed Sarari ta kai wa shugaban hukumar ta tace finafinai. Bayanin wanda yake ƙunshe a wata takardar sanarwa ga manema labarai…