Rahoto

Har ƙasar Saudiyya muna aikin ciyar da abinci – Hajiya Hannatu

Har ƙasar Saudiyya muna aikin ciyar da abinci – Hajiya Hannatu

Daga MUHAMMADU MUJJITABA a Kano Hajiya Hannatu Tijjani Haruna Shugabar gidan abinci na 7:30 dake Kano, ta bayyana cewa daga kafuwar wannan gida ta horas da dubban mata sana’o'i da irin wannan aiki na gidan abinci kyauta da kuma samar wa mutane musamman matasa maza da mata sama da 3,000 domin su dogara da kansu. Hajiya Hannatu ta ce yanzu haka tana tare da wasu, inda wasu kuma suka buɗe nasu don tsayawa da ƙafafuwansu sakamakon horon da suka samu a Kiminu Food. "Don haka ina farin ciki da samun wannan dama daga Ubangiji," inji ta. Hajiya Hannatu Tijjani Haruna…
Read More
Gwamna Dauda Lawal ya ƙuduri aniyar kafa rundunar ‘yan bijilanti a Zamfara

Gwamna Dauda Lawal ya ƙuduri aniyar kafa rundunar ‘yan bijilanti a Zamfara

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Gwamnatin Jihar Zamfara ƙarƙashin Gwamna Dauda Lawal ta bayyana cewa ta tayar da azama wajen yaƙi da 'yan bindiga da sauran miyagun ayyuka a duk faɗin jihar, inda ta ce za ta samar da runduna ta musamman don tabbatar da tsaro a duk faɗin jihar.  Gwamna Lawal ya bayyana haka ne a ranar Laraba yayin da ya ke bayani game shirin da gwamnatin ta yi na zaƙulo wasu matasa daga Ƙananan Hukumomin jihar 14, waɗanda za su yi aikin samar da tsaro a Hukumar tsaron da gwamnatin za ta kafa mai suna 'Community Protection Guards (CPG),…
Read More
An yi jana’izar Sheikh Yusuf Ali a Kano

An yi jana’izar Sheikh Yusuf Ali a Kano

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Allah Ya yi wa fitaccen malamin addinin Musulunci a Jihar Kano, Sheikh Dokta Yusuf Ali rasuwa. Sheikh Dokta Yusuf wanda shi ne Sarkin Malaman Gaya ya rasu ne a daren Lahadi bayan ’yar gajeriyar rashin lafiya, yana da shekaru 73. Ɗan marigayin, wanda ɗan siyasa ne, Muslihu Yusuf Ali ya shaida wa Blueprint Manhaja cewa, an yi janaizar mahaifin nasa a ranar Litinin da Azahar a Masallacin Murtala da ke kusa da titin Gidan Zoo. Shehin malamin ya gudanar da rayuwarsa ta aikin gwamnati a matsayin alƙali, inda ya jagorancin kotunan Shari’ar Musulunci daban-daban…
Read More
Kogi, Imo, Bayelsa: Gobe za a gwada ‘imanin’ gwamnatin Tinubu

Kogi, Imo, Bayelsa: Gobe za a gwada ‘imanin’ gwamnatin Tinubu

•Zaɓen farko tun bayan kafuwar gwamnatinsa Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Kimanin masu kaɗa ƙuri’a miliyan 5.2 ne za su fito a ranar 11 ga Nuwamba, 2023 don zaɓen gwamnoni a jihohin Bayelsa, Imo da Kogi. Adedayo Akinwale, ya yi nazari kan matakin shirye-shiryen alƙalan zaɓe, Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa. Yayin da zaɓen gwamnan jihar Bayelsa da Kogi da kuma Imo ke ƙara ƙaratowa a ranar 11 ga watan Nuwamba, jimillar mutane 5,409,438 da suka yi rajista a jihohin uku ke shirin zaɓar sabbin shugabannin zartarwa na jihohin uku. Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa…
Read More
Mataimakin Gwamnan Kebbi ya yi kira a ƙara ƙaimin tsaro kan iyakoki

Mataimakin Gwamnan Kebbi ya yi kira a ƙara ƙaimin tsaro kan iyakoki

Daga JAMIL GULMA a Kebbi  Mataimakin Gwaman jihar Kebbi Sanata Umar Abubakar Tafidan Kabi ya yi kira ga hukumar kula da kan iyakokin Nijeriya da su ƙara ƙaimi wajen samar da tsaro kan iyakokin. Ya yi wannan kiran a garin Sakkwato ranar Talatar da ta gabata a wajen wani taron ƙara wa juna sani da aka shirya don daƙile ayyukan ta'addanci a kan iyakokin ƙasashen da jihohin da ke maƙotaka da Nijeriya. Sanata Umar Tafida wanda shi ne ya jagoranaci shi rin ya ce ba shakka ƙirƙiro wannan kwamiti zai zaƙulo hanyoyin samar da tsaro da  zai taimaka wajen magance…
Read More
An kashe masu garkuwa da mutane da ceto mutum huɗu a Kebbi

An kashe masu garkuwa da mutane da ceto mutum huɗu a Kebbi

Daga JAMIL GULMA a Kebbi  A wata arangama tsakanin wani gungun 'yan ta'adda da sojojin bataliya ta ɗaya da ke Birnin Kebbi tare da haɗin gwiwa da 'yan sakai sun samu nasarar kashe 'yan ta'adda da dama tare da ƙwato mutane huɗu da aka yi garkuwa da su a jejin Suru da ke jihar Kebbi. Kamar yadda mai bai wa gwamnan jihar Kebbi shawara kan tsaro Alhaji Abdulrahman Usman ya bayyana, an yi ba-ta-kashi tsakanin jami'an tsaro tare da 'yan sa kai da kuma ɓarayin daji a wata maɓoyarsu da ke  kan tsaunin Bangi a bayan garin Suru inda aka…
Read More
Nijar: An bankaɗo sabbin bayanai kan zargin Bazoum da yunƙurin tserewa

Nijar: An bankaɗo sabbin bayanai kan zargin Bazoum da yunƙurin tserewa

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Hukumomin shari’ar jamhuriyar Nijar sun sanar cewa binciken da suka gudanar ya bada damar gano wasu ƙarin bayanan da ke gaskanta zargin yunƙurin tserewar Shugaba Mohamed Bazoum da iyalinsa. Sun ce sun kama kuɗaɗe da dama da wasu tarin kayayyaki a fadar ta hamɓararren shugaban. Yayin da ya ke yin bayani a gidan talabijin ɗin RTN mallakar gwamnatin Nijar, mai shigar da ƙara a Kotun Ɗaukaka Ƙara ta birnin Yamai, Salissou Chaibou, ya ayyana cewa bayanan da suka tattara sun gano cewa an ɗauki hotunan barikin dogarawan fadar shugaban ƙasa da suke zargin hamɓararren shugaban…
Read More
Masarautar Argungu ta ɗaura ɗamarar yaƙi da masu tauye ma’auni

Masarautar Argungu ta ɗaura ɗamarar yaƙi da masu tauye ma’auni

Daga JAMIL GULMA a Kebbi Masarautar Kabin Argungu da ke jihar Kebbi ta ɗaura ɗamarar yaƙi da masu tauye ma'auni kan harkokin sayar da abinci a kasuwanni da ke yankin wannan masarautar. Alhaji Abubakar Yaya shi ne Sarkin Bakin Kabi kuma shugaban gudanar da bincike tare da ɗaukar matakin ladabtarwa ga duk wanda aka samu yana tauye ma'auni. A zantawarsa da wakilinmu a cikin rangadin da ye je a kasuwar Bachaka da ke kan iyakar Nijeriya da Jamhuriyar Nijar ya bayyana cewa ba su yi ƙasa a gwiwa ba wajen yaƙi da masu tauye ma'auni ba saboda wannan aikin ba…
Read More
Mutum biyu sun tsere daga gidan yarin Katsina

Mutum biyu sun tsere daga gidan yarin Katsina

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Wani da ake zargin ɗan fashi da makami ne kuma carawon mota ya tsere daga gidan gyaran hali da ke Katsina. Ana tuhumar ɗaya daga cikin waɗanda ake zargin, Abba Kala da kitsa ayyukan fashi da sace-sacen motoci a Katsina, Filato da sauran jihohin da ke makwabtaka da su. An ce, Kala ya yi amfani da wayarsa ne a lokacin da ake tsare da shi a gidan gyaran hali da ke Katsina wajen shirya wani manaƙisu da aka yi na kwace mota. Kwamandan hukumar gidan yarin ta Katsina Muhammad Abdulmumini Haruna ya tabbatar da faruwar lamarin.…
Read More
Waliyyan ango sun nemi a mayar musu da sadaki don su maida inda aka aro

Waliyyan ango sun nemi a mayar musu da sadaki don su maida inda aka aro

Daga AISHA ASAS  Idan ba ka mutu ba, aka ce komai kana gani. Wani sabon salo, wai Bature da feƙe. A ranar Larabar da ta gabata a Jihar Sakkwato a wata unguwa da ake kira Zoramawa aka yi taro na ji da gani da ƙudirin neman auren wata yarinya da saurayinta da suka jima su na yin soyayya.  Taron da ya ɗauki ilahirin dangin yarinyar lokaci wajen shiri na  kwalliya da kuma kayan abincin da aka shirya don tarbon dangin ango, waɗanda suka haɗa da lafiyayyun kaji da makusantan uwar amarya suka tabbatar kowacce ɗaya daga ciki an siye ta…
Read More