Labarai

Zan fifita matsalolin ‘yan Nijeriya kan komai – Peter Obi yayin da aka fara yaƙin neman zaɓen 2027

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyar NDC, Peter Obi, ya buɗe yaƙin neman zaɓensa a hukumance na takarar kujerar shugaban ƙasa a babban zaɓen 2027 a hukumance, inda ya yi alƙawarin mayar da ababen da ke damun 'yan Nijeriya na yau da kullum a matsayin jigon yawon neman zaɓen nasa. Obi ya bayyana haka ne a birnin Onitsha da ke Jihar Anambara, inda ya ƙalubalanci sauran 'yan takara da su fito su kare tarihin ayyukansu na baya da yin bayanin abin da ya sa suka cancanci jagorancin Nijeriya. Ya ce, kada a riƙa tilasta…
Read More
‘Yan sanda sun ƙaddamar da yaƙi da bangar siyasa a Katsina

‘Yan sanda sun ƙaddamar da yaƙi da bangar siyasa a Katsina

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina Rundunar 'yan sanda sun ƙaddamar da yaƙi da bangar siyasa da laifuka ta amfani da yanar gizo da sauran manyan laifuka a Katsina. Kwamishinan 'yan sanda na Jihar Katsina CP Ali Umar Fage ya sanar da haka a lokacin da yake buɗe taron ranar matasa na duniya a Katsina. Kwamishinan wanda mataimakin kwamishinan 'yan sanda na sashin bincike DCP Aminu Gusau ya wakilta yi gargaɗi duk wanda aka samu yana ɗaukar nauyi ko amfani da matasa wajen bangar siyasa,"zamu yi bincike,mu kama da gurfanar da duk wanda muka kama a gaban kuliya. CP Ali Umar…
Read More

Tinubu ya buɗe yaƙin naman zaɓe da caccakar ‘yan adawa, ya kira Aregbesola da ‘rabin albashi’, Atiku kuma ‘jahili’

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Yayin da aka kaɗa gangar siyasar zaɓukan 2027, Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya buɗe yaƙin neman zaɓensa da caccakar 'yan adawa, inda ya soki tsohon gwamnan Jihar Osun, Rauf Aregbesola da tsohon mataimakin shugaban ƙasa kuma ɗan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyar ADC, Atiku Abubakar kan matsayar siyasa. Tinubu ya yi waɗannan kalamai ne a ranar Alhamis yayin karɓar baƙuncin Gwamna Ademola Adeleke a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja, kwanaki kaɗan da Adeleke ya sake lashe zaɓen gwamnan Osun da aka gudanar a ranar 15 ga Agusta. A ranar 19 ga Agusta ne…
Read More

Gwamnatin Tarayya ta bada hutun Mauldin 2026

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranar Talata, 25 ga Agusta, 2026 a matsayin ranar hutun Mauldin 2026 domin karrama lokacin zagayowar haihuwar fiyayyen halitta Annabi Muhammad SAW. Ministan Harkokin Cikin Gida, Dakta Olubunmi Tunji-Ojo ne ya bayyana haka a yau Jumma'a a wata sanarwa da ya fitar da hannun Babbar Sakatariyar ma'aikatar, Dakta Magdalene Ajani. Ministan ya taya al'ummar Musulmin Nijeriya da wasu sassan duniya murnar zagayowar lokacin, yana mai kira a gare su da su yi amfani da damar hakan wajen nuna tasirin karantarwar Annabi Muhammad a harkokin rayuwarsu na yau da kullum. Ya…
Read More
An karrama Dakta Margaret da lambar yabo ta kwamishiniya mafi hazaƙa a Nijeriya

An karrama Dakta Margaret da lambar yabo ta kwamishiniya mafi hazaƙa a Nijeriya

Daga JOHN D. WADA a Lafiya An karrama kwamishiniyar muhalli da albarkatun ƙasa na gwamnatin jihar Nasarawa gimbiya Dr. Margaret Elayo da lambar yabo na musamman wato kwamishiniya wace tayi zarra a ƙwarewa da aiki tuƙuru da kuma hidima na musamman ga mutane. An bai wa kwamishiniyar wannan karramawar ne a wani babban taro da Arewa Media Publications ta shirya a ranar Alhamis na makon da ake ciki inda kuma har aka ba ta lambar yabo na International Merit Award for Excellence in Leadership a turance ta shekarar 2026. Wato dai hakan na nufin kamar yadda ake ce wa ne…
Read More
Gwamna Raɗɗa zai cigaba da tallafa wa Katsina United

Gwamna Raɗɗa zai cigaba da tallafa wa Katsina United

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Raɗɗa, ya sake jaddada ƙudirin gwamnatinsa ta cigaba da tallafa wa ƙungiyar Katsina United, tare da bunƙasa harkokin wasanni da ƙwarewar matasa a jihar. Gwamnan ya bayyana hakan ne ranar Alhamis lokacin da ya karɓi baƙuncin shugaban hukumar ƙwallon ƙafa ta Najeriya (NFF), Alhaji Ibrahim Musa Gusau, da sauran jami’an hukumar a fadar gwamnatin Jihar Katsina. Gwamna Raɗɗa ya ce gwamnatinsa za ta ci gaba da samar da yanayin da zai bai wa matasa damar haɓaka ƙwarewarsu a wasanni, yana mai cewa ƙwallon ƙafa na taka muhimmiyar rawa wajen haɗa kan matasa da kuma…
Read More

‘Yar Gombe ta lashe gasar Musabaƙar Al-Ƙur’ani a Saudiyya, ta samu kyautar miliyan N120

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Wata 'yar asalin Jihar Gombe mai suna Maryam Ibrahim Ɗan'azumi ta yi nasarar lashe gasar Musabaƙar karatun Al-Ƙur'ani Mai Girma na Sarki Abdulaziz karo na 46 da aka gudanar a ƙasa Mai tsarki ta Saudiyya. Maryam, wadda ɗaliba ce a makarantar Abubakar Siddiq Community Islamic School for Quranic Memorisation, da ke unguwar Herwagana a cikin garin Gombe, ta wakilci Nijeriya ne a gasar a rukunin mahaddata Ƙur'ani izufi 60, Tajwidi da Tafsirinsa. Ta yi nasarar zuwa ta ɗaya a cikin ɗalibai daga ƙasashe da dama, abin alfaharin da ya biyo bayan hazaƙa da ƙoƙarinta…
Read More

An buƙaci Akanta Janar ya binciki EFCC bisa tsare ɗalibar ajin ƙarshe a BUK, Maryam Shehu

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Lauyan kare 'yancin ɗan-adam, Abba Hikima, ya kirayi Antoni Janar na Ƙasa (AGF), da ya gaggauta shiga tsakani cikin lamarin Maryam Isah Shehu, wadda ɗalibar ajin ƙarshe ce ta Jami'ar Bayero da ke Kano, yana mai bayyana tsawaita cigaba da tsare ta da Hukumar Hana yi wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Ta'annati EFCC, ke yi a matsayin saɓa wa doka da hukunce-hukuncen dokokin 'yancin ɗan-adam na Nijeriya. A wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Soshiyal Mediya a ranar Alhamis, Abba Hikima ya caccaki salon yadda EFCC take gudanar da al'amarin ɗalibar, inda ya…
Read More

An ƙaddamar da shirin dashen bishiyoyi 22,000 a Kano da Jigawa

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja An ƙaddamar da shirin dasa bishiyoyi guda 22,000 a sassan jihohin Kano da Jigawa a wani yanayi da bunƙasa lamuran kula da muhalli domin walwalar al'umma. Kwalejin Tarayya ta Ƙere-ƙeren kayan Fasahar Noma da ke Kano tare da haɗin-gwiwar gwamnatin jihar Kano, Gidauniyar British American Tabaco Nigeria Foundation da kamfanin Ahalson Nigeria Limited da masu harkar samar da iri da kayan gona sune suka haɗu don ƙaddamar da wannan shiri. Wannan dai wani wani yunƙuri ne na rage tsananin zafin rana da ake fama da shi a sassan faɗin jihohin. A wata hira da…
Read More
Gwamna Raɗɗa ya amince da naɗin Masa’ud Banye a matsayin muƙaddashin shugaban ma’aikata na Katsina

Gwamna Raɗɗa ya amince da naɗin Masa’ud Banye a matsayin muƙaddashin shugaban ma’aikata na Katsina

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina Gwamnan Jihar Katsina ya amince da naɗin Masa'ud Al'mustapha Banye a matsayin shugaban ma'aikata na riƙo a Jihar Katsina. Naɗa Masa'ud ya biyo bayan ajiye aikin da tsohon shugaban ma'aikata Alhaji Falalu Bawale bayan ya shafe shekara 35 a aikin gwamnatin Jihar. A wata takardar sanarwa ɗauke da sanya hannun sakataran gwamnati Barista Abdullahi Garba Faskari,ya bayyana naɗin a wani ƙoƙari na inganta aikin gwamnati da zai daidaita da shirin gwamnatin Dikko Raɗɗa na 'RENEWED HOPE'. Abdullahi Faskari ya taya Masa'ud Banye murnar samun wannan muka tare da kira a gare shi da ya yi…
Read More