16
Aug
Daga AISHA ASAS Sabon iƙirari kan mutuwar jarumar Nollywood, Temitope Osoba, ya sake jawo hankalin jama’a bayan wanda ya ce shi ne wanda za ta aura ya bayyana cewa an sanar da shi mutuwar jarumar ne a wani ofishin ’yan sanda da ke Ikorodu a Legas. Jaruma Osoba ta rasu tana da shekaru 40, kuma labarin mutuwarta ya fara yaduwa ne a ranar Laraba, 5 ga Agusta. Jarumar ta taɓa fitowa fili ta bayyana wa jama’a irin gwagwarmayar da ta yi da cutar kansa, bayan an gano tana fama da cutar kuma aka yi mata tiyata. Saboda haka, bayan rasuwarta,…
