Labarai

Ranar Hausa ta duniya: Sarakuna da masana sun nemi kare harshen Hausa

Ranar Hausa ta duniya: Sarakuna da masana sun nemi kare harshen Hausa

Daga ABUBAKAR A BOLARI Gombe Manyan baƙi da masu ruwa da tsaki a harkar raya harshen Hausa sun jaddada muhimmancin kare harshen da al’adun Hausawa, tare da kira ga al’umma, musamman matasa, da su rungumi harshen domin tabbatar da ɗorewarsa a wannan zamani na fasahar sadarwa. Sun bayyana hakan ne a wajen bikin Ranar Hausa ta duniya, wanda ya haɗa manyan baƙi daga ciki da wajen Jihar Kano, ciki har da sarakuna, malamai, masana da shugabannin al’umma masu ruwa da tsaki wajen bunƙasa harshen Hausa da kare al’adun Hausawa. Da yake gabatar da jawabinsa, Mai Martaba Ambasada Alhaji Ibrahim Haruna,…
Read More
Ƙungiyoyi 100 a Zamfara na goyon bayan Tinubu da Gwamna Lawal su zarce

Ƙungiyoyi 100 a Zamfara na goyon bayan Tinubu da Gwamna Lawal su zarce

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Hukumar kula da harkokin siyasa ta Jihar Zamfara ta gudanar da taron wayar da kan jama'a na kwanaki biyu da kuma gangamin goyon bayan Gwamna Dauda Lawal da Shugaba Bola Ahmed Tinubu a karo na biyu a shekarar 2027 a Zamfara. Bitar ta gudana yau Laraba a Gidan Alh. Umaru Shinkafi, Unguwar Gwaza, kusa da Hedikwatar 'yan sanda, Gusau. Da yake jawabi a lokacin taron, mai ba da shawara na musamman ga gwamna kan harkokin Siyasa, Hon. Alhaji Nura Sani Abdullahi, ya ce an tsara wannan gangamin ne don ƙarfafa nasarorin da Gwamna Lawal da…
Read More

‘Yan bindiga sun halaka ɗan uwan ministan Tinubu a Neja

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja An zargi wasu 'yan bindiga da halaka wani yayan Ƙaramin Ministan Noma da Tsaron Abinci, Aliyu Sabi Abdullahi a Jihar Neja. Marigayin Mai Gari ne a ƙauyen Galla da ke Masarautar Borgu a Ƙaramar Hukumar Borgu. A ranar Litinin, 24 ga Agusta, 2026 ne maharan suka afka wa jama'a a fadarsa, lamarin da ya jefa al'ummar ƙauyen cikin firgici. A cewar rahotanni, majiyoyi masu masaniya kan al'amarin sun ce da fari basaraken ya gargaɗi 'yan bindiga da su nisanci ƙauyen muddin suna son zaman lafiya. An bayyana wannan gargaɗi a matsayin karan tsaye ga…
Read More
Hausawa mutane ne masu son haɗin kai da ci gaban Najeriya – Tinubu

Hausawa mutane ne masu son haɗin kai da ci gaban Najeriya – Tinubu

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ce Hausawa na taka muhimmiyar rawa wajen haɗin kai da ci gaban Najeriya, tare da yaba wa gudunmawar da al'ummar ke bayarwa wajen bunƙasa ƙasar. Tinubu ya bayyana haka ne yayin da yake taya al'ummar Hausawa murnar ranar Hausa, wadda ake gudanarwa a masauratar Daura, da ke jihar Katsina cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X. Shugaba Tinubu ya ƙara da cewa harshen Hausa ya bunƙasa sosai, kuma ya zama wani muhimmin harshen sadarwa da kasuwanci a sassa daban-daban na duniya. Shugaban ya kuma taya ɗaukacin al'ummar Hausawa murna, yana mai…
Read More

Gwamnatin Trump ta dakatar da bada bizar Amurka ga kowacce ƙasa

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Gwamnatin Shugaba Donald Trump na Amurka ta dakatar da bayar da baki ɗaya bizar shiga ƙasarta ga masu buƙata yayin da ofisoshin jakadancinta suka fara bada sabon horo ga jami'an harkar jakadanci. Fadar shugaban ƙasar ne ta tabbatar da haka a ranar Talata, inda ta ce za a yi gyara kan waɗanda suke aiki akansu domin bai wa ofishin difulomasiyyarsu damar shiga horon. Gwamnatin ta kuma ce, matakin wani ɓangare ne na ƙoƙarinta akan ƙarfafa ayyukan tantancewa da inganta tsaron ƙasar. Wani kakakin fadar ya ce aikin horon zai taimaka wa jami'an ofisoshin jakadanci…
Read More

Hukumar tace finafinai za ta hukunta furodusoshin ‘Living in Colors’ kan fitarwa ba tare da amincewarta ba

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Hukumar Tace Finafinai da Bidiyo ta Ƙasa (NFVCB) ta ce za ta ɗauki matakin doka akan furodusoshin fim ɗin Living in Colors bisa shirin fitar da fim ɗin ba tare da sahalewar hukumar ba. Living in Colors wani fim da aka yi akan wasu matasa su biyar da ke zama a gida ɗaya a Legas, sannan suka nemi cigaba da zaman daduro a tsakaninsu ba tare da la'akari da jinsi ba. A wata sanarwa da Shugaban NFVC, Dakta Shuaibu Husseini ya fitar, hukumar ta koka kan yadda ba a gabatar mata da fim ɗin…
Read More

Tinubu ya umarci hukumomin tsaro su ceto masallatan Neja da aka sace

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Shugaba Bola Tinubu ya umarci rundunonin soji, 'yan sanda, hukumar tsaro ta farin kaya DSS da sauran hukumomin tsaro da na leƙen asiri, da su gaggauta ƙaddamar da atisayen ceto mutanen nan masu yawa da aka sace a Jihar Neja. Wannan umarni na zuwa ne bayan garkuwa da halaka wasu fararen hula daga ɓangaren 'yan ta'adda a jihar, inda shugaban ƙasar ya koka akan aukuwar iftila'in. A wata sanarwa da Kakakin Shugaban ƙasa Bayo Onanuga ya fitar a ranar Talata, Shugaban ya bayyana masu hannu a mummunan harin a matsayin maƙiya zaman lafiya da…
Read More

Sojoji sun ceto mutum 14 bayan daƙile yunƙurin garkuwa a Zamfara

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Dakarun tsaron Shiyya ta 2 na Atisayen FANSAR YAMMA, sun yi nasarar daƙile wani yunƙuri da yin garkuwa da mutane, sannan sun ceto mutum 14 yayin atisayen a Ƙaramar Hukumar Tsafe da ke Jihar Zamfara a ranar Talata. Wata majiyar tsaro ta shaida wa wakilinmu cewa, an gudanar da atisayen ne a ranar Talata, 25 ga Agusta bayan samun wani bayani na sirri kan lamuran ababen zargi a yankin ƙauyen Magazu. Akan haka ne rundunar ta tura jami'an tsaro yankin, inda suka yi arangama da maharan da ke ƙoƙarin sace wasu fararen hula ciki…
Read More

Ka daina tsoma baki a idan ‘yan siyasa na magana – Amaechi ga Sowore

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Wani fagen tattaunawar harkar siyasa a babban taron Ƙungiyar Lauyoyi ta Ƙasa (NBA) karo na 66 a Fatakwal, Jihar Ribas ya koma cacar baki bayan ɗan takarar shugaban ƙasa a jam'iyyar AAC, Omoyele Sowore ya ƙalubalanci tarihin siyasar 'yan siyasar da suka riƙe muƙaman gwamnati a baya. Ana haka ne tsohon Gwamnan Jihar Ribas kuma tsohon Ministan Sufuri Rotimi Amaechi, wanda ya wakilci ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar ADC, Atiku Abubakar a taron, ya mayar da martani kan sukar. Ya ƙalubalanci Sowore da ya bayyana ƙwarewarsa a fagen shugabanci. An fara musayar kalaman…
Read More

Kano: ‘Yan unguwa sun ƙi karɓar cin hancin N10m don rufa-rufa ga zargin safarar miyagun ƙwayoyi

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Mazauna Unguwar Bajallabe da ke yankin FCE Gate na 1 a garin Kano, sun ƙi amincewa su karɓi wani tayin cin hanci da aka yi zargin ya kai Naira miliyan 10 domin su yi rufa-rufa ga wata mota da ake zargin ta da jigilar miyagun ƙwayoyi. Al'amarin ya faru ne a safiyar ranar Talata bayan 'yan yankin sun gano wata mota ƙirar Golf da ake zargin tana maƙare da haramtattun ƙwayoyi, wadda aka ajiye a gefen wani babur kusa da wani gida da ke unguwar. Kakakin hukumar jami'an yaƙi da sha da fataucin miyagun…
Read More