Babban Labari

Kebbi:  Kamfanonin  haƙar ma’adanai na cin karensu ba babbaka

Kebbi:  Kamfanonin  haƙar ma’adanai na cin karensu ba babbaka

Daga JAMILU GULMA, a Kebbi  Al'ummar yankin garuruwan Libata da Lokon-Uba da Kabiriba da sauran ƙananan ƙauyuka da ke ƙaramar Hukumar Mulki ta Ngaski da ke Jihar Kebbi sun koka bisa ga yadda kamfunnan haƙar ma'adanai a yankin ke cin karen su ba babbaka yayin da aka mayar da al'ummomin yankin ’yan kallo ba tare da wani ihsani ba ko samar da abubuwan more rayuwa ba. Malam Sani Aliyu daya ɗaga cikin matasan yankin kuma mai sana'ar kabu-kabu (acaba)ya bayyana wa wakilinmu cewa, waɗannan mutanen sun daɗe suna cin karen su ba babbaka a yankin wajen haƙar ma'adanai da su…
Read More
Taron shekara na Blueprint:Nijeriya na buƙatar ninkin naman dabbobi – Jega

Taron shekara na Blueprint:Nijeriya na buƙatar ninkin naman dabbobi – Jega

*Etsu Nupe ya yaba wa Bluprint *Tinubu na da cikakken goyon baya ga ’yancin ’yan jarida, inji Minista Idris *Gwamnatin Tarayya ta ƙalubalanci kiwo sakaka *Kwazo a jagoranci ne ke nuna haƙiƙanin martaba, inji Manajan Daraktan Blueprint Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja An samu gagarumar nasarar gudanar da taron shekara-shekara, wanda kamfanin gungun jaridun Bluerint ke shiryawa a ranar Talatar da ta gabata, inda ƙwararru, masana da masu ruwa da tsaki suka bajekolin basirarsu a taron, wanda ya fi mayar da hankali kan bunƙasa harkokin kiwo a Nijeriya baya ga karrama zaƙaƙuran da suka fi yin fiice a shekarar. …
Read More
Yadda Buhari ya rasu wata 25 bayan mulki

Yadda Buhari ya rasu wata 25 bayan mulki

*Yadda aka yi tururuwar jana’iza da ta’aziyyarsa *Wane ne Muhammadu Buhari *Yadda Buhari ya gudanar da rayuwarsa a gida *Fitattun kalamai bakwai da za a riƙa tunawa da Buhari a lokacin mulkinsa Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Bayan duk wasu jita-jita da aka dinga yaɗawa na ƙarya na bayyana rasuwarsa, a ƙarshe dai tsohon Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari ya rasu a wani asibiti da ke Landan bayan ya sha fama da jinya. A wancan makon ne dai aka yi ta raɗe-raɗin cewa, tsohon shugaba Buhari ya rasu, kamar dai yadda ya faru a tsakanin shekarar 2016 zuwa 2019, a…
Read More
Zaɓen 2015: Ana musayar yawu kan Tinubu da Buhari

Zaɓen 2015: Ana musayar yawu kan Tinubu da Buhari

*Cacekuce ya ɓalle tsakanin Fadar Shugaban ƙasa da ‘yaran’ Buhari *Ba Tinubu ne ya sa Buhari ya ci zaɓe a 2015 ba – Boss Mustapha *Tinubu ne ya buɗe wa Buhari ƙofa — Fadar Shugaban ƙasa *Ba zan juya wa APC baya ba, inji Buhari Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Daga dukkan alamu musayar yawu da cecekucen siyasa ya ɓalle a tsakanin Fadar Shugaban ƙasa da wasu daga cikin manyan magoya bayan tsohon Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari kan rawar da Shugaban ƙsaa mai ci, Bola Ahmed Tinubu, ya taka a zaɓen 2015, wanda ya kai Buhari ga samun nasarar…
Read More
An fara maida yawu kan haɗakar jam’iyyar ADC

An fara maida yawu kan haɗakar jam’iyyar ADC

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Tun a ranar da wasu manyan adawa a Nijeriya suka bayyana samar da haɗaka a Jam’iyyar ADC aka fara mayar da yawu tsakanin ɓangarorin masu ruwa da tsaki a siyasar Nijeriya, musamman jam’iyyun adawa, inda yanayin ke nuni da cewa, ba lallai ne komai ya tafi salim alim, kamar yadda aka yi zato tun farko ba. Wannan ya sanya Blueprint Manhaja ta tattaro akasarin bayanai na abubuwan da suke faruwa daga ayyana haɗakar zuwa haɗa wannan rahoto. Dalilinmu na zaɓar ADC a matsayin jam'iyyar haɗaka, inji su: A ranar Laraba ne manyan ’yan adawar siyasa na…
Read More
Sauye-sauyen da ke cikin sabuwar dokar haraji

Sauye-sauyen da ke cikin sabuwar dokar haraji

*Tinubu ya rattaɓa hannu jiya Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya sanya hannu akan sababbin dokokin haraji guda huɗu, waɗanda suka tsallake karatu a Majalisar Dokoki na ƙasa a baya. Shugaban ƙasar ya yi haka ne a Fadar Shugaban ƙasa dake Abuja, inda aka samu halarcin jagorancin majalisa da wasu 'yan majalisu da gwamnoni da ministoci da mataimakan Shugaban ƙasa. ƙudirorin sun haɗa da na haraji na ƙasa, na tattara haraji na ƙasa, na samar da hukumar kuɗaɗen haraji da kuma na samar da hukumar haɗaka ta haraji, waɗanda aka tantance su a Majalisar…
Read More
2027: Yadda tikitin Tinubu da Shettima ya ɗauki hankali

2027: Yadda tikitin Tinubu da Shettima ya ɗauki hankali

*Jita-jita da zarge-zarge sun taka rawar dambarwar *Tinubu zai iya warware matsalar kamar a Jihar Legas? Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Duk da cewa, zaɓen 2027 ya rage saura shekara biyu, wani shiri da ake zargin ana yi na jingine Mataimakin Shugaban ƙasa Kashim Shettima a matsayin abokin takarar Shugaban ƙasa Bola Tinubu a zaɓen yana neman raba kan Jam’iyyar All Progressiɓes Congress (APC) mai mulki. Taron da masu ruwa da tsakin Jam’iyyar APC na shiyyar Arewa maso Gabas suka gudanar a Jihar Gombe ranar Lahadin da ta gabata, ya ƙare da rashin jituwa, dutse a hannun riga, yayin…
Read More
Ranar Dimukraɗiyya: Ina murnar ganin jam’iyyun adawa cikin ruɗani – Tinubu

Ranar Dimukraɗiyya: Ina murnar ganin jam’iyyun adawa cikin ruɗani – Tinubu

PDP ta buƙaci 'yan Nijeriya su ƙaurace wa tsarin jam'iyya ɗaya Majalisa ta amince da 'June 12' a matsayin Ranar Jawabin Shugaban ƙasa Siyasa ta fi damun ka maimakon aiki – Obi ga Tinubu Daga SANI AHMAD a Abuja A jiya Alhamis ne Shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya ce, jam’iyyarsa ta APC ba za ta rufe ƙofarta ga ’yan jam’iyyar adawa da suka zaɓi koma wa jam’iyyar APC ba, yana mai cewa, bai damu da rikicin da ke faruwa a jam’iyyun adawar ba ko taimaka musu wajen gyara matsalolinsu, inda ya ƙara da cewa, abin farin ciki ne ma…
Read More
Tsadar raguna ta sa magidanta watanda

Tsadar raguna ta sa magidanta watanda

*'Yan kasuwa sun koka da tsadar Daga JAMIL GULMA a Kebbi  Layya dai wata ibada ce ta yanka dabbobi daga ranar goma ga watan goma sha biyu (Zul-Hajji) zuwa goma sha biyu ga watan da suka haɗa da yanka rago ko tinkiya da raƙumi ko rakuma da  Sa ko saniya da akuya ko bunsuru (ɗan taure) da aka ce ta samo asali ne tun lokacin Annabi Ibrahim Alaikissalam da Allah ya umarce shi da ya yanka ɗan sa Annabi Isma'il Alaihissalam daga baya kuma Allah ya fanshe shi da rago. Ita dai wannan ibadar sunnah ce mai ƙarfi da aka…
Read More
Manyan ƙasa sun yi tsokacin shekara biyun Tinubu

Manyan ƙasa sun yi tsokacin shekara biyun Tinubu

A ƙara haƙuri da tsare-tsaren Tinubu – Buhari Manufofin attajirai ne, ba na talakawa ba – Atiku Sauye-sauyen kasuwaci abin a yaba ne – BUA Daga NASIR S. GWANGWAZO a Abuja Kamar yadda aka yi tsammani, yayin da Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya cika shekara biyu akan karagar mulki a jiya Alhamis, 29 ga Mayu, 2025, masu ruwa da tsaki sun tofa albarkacin bakinsu kan rawar da gwamnatinsa ta taka a tsawon wannan lokaci. Cikin waɗanda suka yi tsokaci akwai wanda ya gada, tsohon Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari da jagoran ’yan adawa ƙasar kuma tsohon Mataimakin Shugaban ƙasa, Alhaji…
Read More