Ra’ayi

Me ya sa ‘yan siyasa ke mantawa da mata idan sun samu gwamnati?

Me ya sa ‘yan siyasa ke mantawa da mata idan sun samu gwamnati?

Mata a Nijeriya sun koka da yadda ake mantawa da su bayan ’yan siyasa sun samu gwamnati duk da fitowar da suke ƙwansu da ƙwarƙwata wajen kaɗa ƙuri’a a yayin zaɓe. Wannan koke na matan na zuwa ne a daidai lokacin da ake daf da gudanar da zavukan ƙasar na 2023. Wannan matsala ta rashin damawa da mata a siyasa abu ne da ya daɗe yana ciwa wasu mata tuwo a ƙwarya ganin yadda suka ce ana watsi da su a lokacin da siyasa ta yi daɗi. Matan na cewa wataƙila hakan baya rasa nasaba da rashin ba su cikakkiyar…
Read More
Farashin litar fetur ta zama ‘kasuwa ta yi halinta’!

Farashin litar fetur ta zama ‘kasuwa ta yi halinta’!

Daga NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Gaskiya yanzu ba wanda zai ce ga tsayeyyen farashin litar man fetur a gidajen man fetur a Nijeriya kawai ya danganta ga inda mutum ya ke da zama wato a cikin birane ne ko a manyan hanyoyin da ke tsakanin jihohi. Duk wata tsadar da a ka ambatawa mai ban tsoro ta tabbata. Dama can ai a na maganar in an janye dukkan tallafi litar fetur za ta haura Naira 300. Yanzu wannan ba sabon labari ba ne a wajen masu sayan man. Wato lamarin nan ya zama gidan kowa na hulɗa da fetur kai tsaye…
Read More
Gargaɗi akan zaɓen 2023

Gargaɗi akan zaɓen 2023

A daidai lokacin da ake tunkarar babban zaɓen ƙasar na 2023, Majalisar Ɗinkin Duniya (UN), Tarayyar Turai (EU) da Ƙungiyar Raya Tattalin Arzikin Ƙasashen Yammacin Afirka (ECOWAS) sun yi gargaɗi game da tashe-tashen hankula a lokacin zaɓe da sauran laifuffuka da ka iya kawo cikas ga gudanar da zaɓen. Ƙungiyoyin sun yi magana kan illolin tashe-tashen hankula a lokacin zaɓen da kuma yin gargaɗin cewa illar na iya yin muni ga yankin da ma nahiyar Afirka bakiɗaya. Sun kuma jaddada cewa idan aka samu tarzoma a yayin zaɓen, babu wata ƙasa a yammacin Afirka da za ta iya shawo kan…
Read More
Garba Shehu: Murucin kan dutse

Garba Shehu: Murucin kan dutse

Daga KWAMARED IBRAHIM ABDU ZANGO Gaskiyar lamari na yaba da ƙwazon Malam Garba Shehu wanda yanzu yake mataimaki na musamman ga fadar shugaban ƙasa malam Muhammadu Buhari a matsayin mai watsa labarai na musamman wato dai a hausance, mai yaɗa labarai wanda idan ka ji shi to da izinin shugaban ƙasar ya yi. Malam Garba Shehu ba shi kaɗai ba ne akwai wani shahararren ɗan jarida shi ne mai faɗin wasu abubuwa wanda suka danganci ƙasashen waje shi ma dai da ka ji shi, to da yawun shugaban ƙasa ya yi, wato shi ne, Mista Adeshina. Gaskiya a duk masu…
Read More
Yadda ƙabilanci zai yi tasiri a zaɓen 2023 a Nijeriya

Yadda ƙabilanci zai yi tasiri a zaɓen 2023 a Nijeriya

Daga DATTI ASSALAFIY A yanzu haka, zancen da ake yi dai haɗakar ƙungiyar Yarbawa ta Duniya sun fitar da sharuɗɗan ƙabilanci masu tsauri da suke so ɗan takarar APC Bola Tinubu ya ɗauka ya yi musu alƙawarin zai cika kafin su goyi bayansa a zabe mai zuwa. Sharuɗɗan su ne: Tabbacin samun tsaron yankin Yarabawa ta hanyar ba wa ƙungiyarsu ta tsaro mai suna AMATEKUN makaman tsaron da za su yi amfani da shi.Gyarawa ko rusa tsarin shiyya-shiyya guda 6 na ƙasar Nijeriya (Geo Political zones), tsarin da zai fitita yankinsu na Yarbawa.Haɗe yarukan da suke da dangantaka da Yarbawa…
Read More
Cin amanar makusanta ga cin zarafin ‘ya’ya mata

Cin amanar makusanta ga cin zarafin ‘ya’ya mata

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Na samu halartar wani taron ƙaddamar da littafin da wata matashiyar marubuciya Aisha Hamza Kallari ta wallafa da harshen Turanci, mai suna Shackles of Abuse, wato Sarƙaƙiyar Cin Zarafi, labarin bautar da 'ya'ya mata cikin lalata. Ko da yake ba ina son yin sharhi kan littafin ba ne, sai dai labarin da jigon littafin ya tavo ne ya tava zuciyata, kuma na ga ya dace mu yi nazari a kansa cikin wannan mako. Labaran da ke cikin wannan littafin suna da tsoratarwa da firgitarwa ainun, musamman irin yadda marubuciyar ta riƙa kwatanta halin da ta samu…
Read More
So kaɗai ba ya iya riƙe aure

So kaɗai ba ya iya riƙe aure

Daga AMINA YUSUF ALI Barkanmu da sake haɗuwa a wani makon! Duk da dai Hausawa sun ce: "so Aljannar Duniya". Haka kuma sun ce; "so gishirin rayuwa". To amma masu dabara, zaman lafiya da maslaha da dacewar halayya suka zaɓa. Matasa kada ku yaudaru da waɗancan kalamai. Duk kuwa da zaqinsu kamar zuma sabuwa! Ku buɓe idanu da kunnuwa ku kalli gabanku. Ku guje wa yin aure don so kawai. Idan ka zavi dacewar halayya da tsarin rayuwa sai ka ga bayan an yi aure, soyayyar ta ginu a hankali. Ba a ce kada a yi auren soyayya ba, kuma…
Read More
Zaɓe bayan cika shekaru 24 a wata mai zuwa

Zaɓe bayan cika shekaru 24 a wata mai zuwa

Daga NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Tun da a ka fara mulkin dimokraɗiyya a Nijeriya wanda ya samo asali daga samun ’yancin ƙasar a 1960 an samu mulkin farar hula a zaɓuka daban-daban inda gabanin zaɓen 1999 an samu shigowar sojoji ne da su ka kifar da gwamnatin farar hula. A ranar 15 ga watan Janairun 1966 sojoji ’yan zubar da jini sun kifar da gwamnatin firaminista Sir Abubakar Tafawa Balewa wanda hakan ya jawo yankewar mulkin farar hula har sai a 1979 inda a ka gudanar da zave marigayi Shehu Shagari ya lashe a qarqashin jam’iyyar NPN mai alamar masara. A…
Read More
’Ya’ya na kowa ne, a daina cin zarafin ’ya’yan riƙo

’Ya’ya na kowa ne, a daina cin zarafin ’ya’yan riƙo

Assalam alaikum. Ina miƙa saƙon gaisuwa da ban bajiya ga dukka ma'aikatan jaridar Blueprint Manhaja, Allah Ya albarkaci wannan jarida, Amin. Wata babbar matsala na tasowa da ta shafi yadda wasu mutane ke ɗaukar 'ya'yan da ba nasu ba na cikinsu, a wulaƙance, musamman ma dai 'ya'yan riƙo da suke ɗauko su daga ƙauye ko gidajen 'yan uwa, don su taimaka musu, ko kuma marayu ne da iyayen su suka rasu. Akwai kuma batun yaran aiki da ake ɗauko su daga ƙauye ko daga gaban iyayen su, don su yi aiki a gidajen masu kuɗi ko ma'aikata, don su taya…
Read More
Siyasar bana: Kada mu sake mu yi zaɓen tumun dare

Siyasar bana: Kada mu sake mu yi zaɓen tumun dare

Daga BELLO MUHAMMAD SHARAƊA Zuwa ga talakawa masu zaɓe. Wannan siyasar da muke yi, Allah ya sani kuma wasu jama'a da muke tare da su, sun san haka, masu fahimta daga lafuzanmu za su gane, niyyarmu da burinmu shi ne yadda sauran al'umma suke amfanar da rayuwarsu ta hanyar ingantaccen tsari na ƙasa, haka muke fata a samu a Nijeriya, a nan duniya mu yi abin kirki, na ƙwarai da alheri, a lahira mu karɓi sakamako a hannun dama. Hukumar zaɓe ta ƙasa INEC ta tsara a duk faɗin Najeriya za ta riƙa ba da bayanai duk sati biyu, daga…
Read More