Ra’ayin Manhaja

Tallafin naira biliyan 600 ga manoma

Tallafin naira biliyan 600 ga manoma

Labarin da aka bayar cewa Gwamnatin Tarayya na shirin bada tallafin sama da naira biliyan 600 don agaza wa manoma abin farin ciki ne. Ba shakka, abin da ya dace ne idan har ana so a faɗaɗa hanyoyin inganta tattalin arzikin ƙasar nan, wanda ya shafe sama da shekara hamsin ya na dogaro da man fetur wajen samun kuɗaɗen shiga. Ministan Aikin Gona Da Raya Yankunan Karkara, Alhaji Sabo Nanono, shi ne ya bayyana labarin a cikin wata sanarwa da Daraktan Yaɗa Labarai na ma’aikatar sa, Mista Theodore Ogaziechi, ya rattaba wa hannu kwanan nan a Abuja. A sanarwar, an…
Read More

Sababbin hafsoshin Buhari

An daɗe ana kira da roƙo ga Shugaba Muhammadu Buhari da ya sauya manyan hafsoshin sojan ƙasar nan masu jagorancin rundunonin tsaro, amma ya na ƙi. Sai da ta kai Majalisar Tarayya ta zartar da ƙudirori a kan lallai ne Shugaban ya kori hafsoshin, amma dai maganar ta wuce ta bayan kunnen sa. Dalilai biyu su ka sanya aka riƙa yi masa wannan kiran. Na farko shi ne, wa’adin hafsoshin ya wuce, har ma ana ganin sun fara cin wa’adin wasu hafsoshin domin tun a cikin 2015 aka naɗa su. Dalili na biyu kuma shi ne gazawar da ake ganin…
Read More