Ra’ayin Manhaja

Batun sake dawo da martabar noma a Nijeriya

Batun sake dawo da martabar noma a Nijeriya

Kamar dai yadda kowa ya sani ne cewa, akwai matuƙar gayar muhimmanci ga Gwamnatin Nijeriya ta sake duba batun bunƙasa harkokin noma a ƙasar nan, duba da rawar da ɓangaren ke takawa wajen ci gaban tattalin arzikin ƙasa da samar da wadataccen abinci. Ayyukan noma su ne ginshiƙi kuma babbar hanyar da za ta iya jure kowace irin kwaramniya ga ci gaban ƙasa tare da al’ummarta baki ɗqaya. Noma babbar abu ce a Nijeriya, ana ma kallon cewa ita ce sana’ar da ta fi kowace sana’a muhimmanci, wacce idan babu ita rayuwar ma sam-sam ba za ta yiwuwa ba. Haka…
Read More
Yaƙi da bautar da yara ƙanana

Yaƙi da bautar da yara ƙanana

Sanarwar da Ƙungiyar Ƙwadago ta Majalisar Ɗinkin Duniya (ILO) ta yi na baya-bayan nan ya nuna cewa, sama da yara miliyan 152 ko kusan ɗaya cikin yara 10 a duniya na fama da tilastawa wajen aure ko yin aikin ƙwadago wanda hakan ba wai kawai abin baƙin ciki ba ne amma har da nuna rashin mutuntaka. Ƙungiyar ta ce, ƙananan yara sama da miliyan 10 ke aiki a matsayin baran gida ko kuma masu hidima a qasashen duniya, wanda ake danganta shi da bauta. Ƙididigar da hukumar ta bayar cikin makon da ya gabata, ya nuna cewa, cikin adadin kashi…
Read More
Dole ne a ɗore da yaƙi da cin hanci da rashawa

Dole ne a ɗore da yaƙi da cin hanci da rashawa

Ranar Alhamis ɗin da ta gabata ne al'ummar duniya suka ware a matsayin ranar yaƙi da cin hanci da rashawa ta duniya. Majalisar Ɗinkin Duniya ta ƙuduri mai lamba 58/4 na ranar 31 ga watan Oktoban shekarar 2003 ta ware ranar 9 ga watan Disamba na kowace shekara a matsayin ranar wayar da kan jama'a game da laifukan da ke kawo cikas ga ci gaba da kuma talauta jama'a. Har ila yau, rana ce ga shugabannin siyasa, gwamnatoci, hukumomin shari'a, ƙungiyoyin fafutuka da qungiyoyin farar hula don sabunta alqawurran da suka ɗauka na kawar da wannan abu da aka gano…
Read More
Buƙatar tsaftace babban titin Abuja zuwa Kaduna

Buƙatar tsaftace babban titin Abuja zuwa Kaduna

Kiran da Majalisar Wakilai ta yi na cewa, shugaban hafsan sojin ƙasa, Laftanar Janar Farouk Yahaya, da Sufeto Janar na ’yan sanda, Usman Baba, ya kamata su magance yawaitar hare-haren ’yan bindiga da masu garkuwa da mutane a kan matafiya a babbar hanyar Abuja zuwa Kaduna da sauran hanyoyin ƙasar nan, duk da cewa an makara, ya dace kuma abin a yaba ne. Majalisar ta kuma umurci dukkanin kwamitocin ta kan harkokin tsaro da su riqa tattaunawa da hukumomin tsaro duk wata tare da bayyana wa shugabanni da ɗaukacin zauren majalisar a kowane wata da kuma wata uku kan abubuwan…
Read More
Batun hana shigo da Alkama daga waje

Batun hana shigo da Alkama daga waje

Kiran baya-bayan nan da Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya yi ga manoman alkama na Nijeriya da su rungumi noman alkama a matsayin hanyar hana shigo da kayan daga ƙasashen waje abin farin ciki ne a cigaban ƙasar nan ta hanyar da ta dace, domin kuwa Nijeriya na kashe kusan dala biliyan 2.2 don biyan ƙananan buƙatun cikin gida a duk shekara. Shugaba Buhari ya yi wannan roƙo ne a wajen ƙaddamar da shirin noman alkama na farko da aka yi a gonakin iri na alkama da ke Kwall a ƙaramar hukumar Bassa a jihar Filato. Ya koka da yadda masu…
Read More
Yawaitar asarar rayuka sakamakon ruftawar gini

Yawaitar asarar rayuka sakamakon ruftawar gini

A wani rahoto daga wani bincike da aka buga a makon da ya gabata an nuna cewa, aƙalla mutane 305 ne suka mutu yayin da mutane 449 suka samu munanan raunuka ta hanyar ruftawar benaye 83 a Nijeriya tun daga shekarar 2013, wanda ya kasance ba wai kawai abin damuwa ba ne amma kuma abin takaici ne. Binciken da wata jarida ta ƙasa ta gudanar ya bayyana cewa, alƙaluman sun nuna ƙarara ga kafafen yaɗa labarai, domin da yawa ba a taɓa jin labarinsu ba. Ya ce, har yanzu Legas ce cibiyar rugujewar gine-gine a Nijeriya inda aka samu rahoton…
Read More
Batun ayyukan madatsun ruwa da aka watsar

Batun ayyukan madatsun ruwa da aka watsar

Ga duk al’ummar da ta ke da muradin mayar da noma wani ginshiƙin tattalin arzikinta, sanin cewa an yi watsi da ayyukan ruwa ko madatsun ruwa kusan 400 abu ne mai matuƙar tayar da hankali. Shugaban kwamitin majalisar dattijan Nijeriya mai kula da albarkatun ruwa, Sanata Bello Mandiya, ne ya bayyana hakan a ranar Talata yayin da ya ke zantawa da manema labarai bayan kammala zaman kare kasafin kuɗi da suka yi da ministan albarkatun ruwa, Injiniya Suleiman Adamu, inda ya koka da cewa da yawa daga cikin madatsun ruwa ba su da wani amfani a ƙasar. Sanata Mandiya ya…
Read More
Ranar hana cin zarafin ’yan Jarida ta duniya

Ranar hana cin zarafin ’yan Jarida ta duniya

Al'ummar duniya baki ɗaya na bikin wannan rana a matsayin ranar kawo ƙarshen cin zarafin ’yan jarida da ma'aikatan yaɗa labarai na duk duniya. Majalisar Ɗinkin Duniya a shekara ta 2013 ne ta zartar da wani ƙuduri a zamanta na 68 tare da ayyana ranar 2 ga watan Nuwamba na kowace shekara a matsayin ranar bikin, inda ta buƙaci ƙasashe mambobin ƙungiyar da su aiwatar da kwararan matakai na daƙile aukuwar lamarin na cin zarafinsu. An zaɓi ranar ne domin tunawa da kisan gillar da aka yi wa wasu ’yan jaridar Faransa biyu, Ghislaine Dupont da Claude Verlon a Mali…
Read More
Gangamin bukukuwan Maulidi

Gangamin bukukuwan Maulidi

Al'ummar Musulmi da dama a Nijeirya sun bi sahun sauran ’yan uwansu a faɗin duniya wajen murna da zagayowar ranar haihuwar Annabi Muhammad (Tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi.) Musulmai da dama sun yi amannar cewa a watan Rabiu'l Awwal, aka haifi Annabi Muhammad (SAW). A irin wannan rana ce Allah (SAW), ya yi wa halittarsa kyautar da ta fi kowacce irin kyauta daraja wato Manzon Allah SAW, kamar yadda Musulunci ya bayyana. Al'ummar Musulmai dai kan yi hidima a wannan lokaci, kamar a Nijeriya musamman a jihohin arewacin ƙasar, makarantun allo ko na Islamiyya kan shirya…
Read More
Batun Naira biliyan 13.3 da aka ware don aikin ‘yan sandan al’umma

Batun Naira biliyan 13.3 da aka ware don aikin ‘yan sandan al’umma

Sanarwar da Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari ya yi kan cewa, ya amince da ware Naira biliyan 13.3, don fara aikin 'yan sanda na al'umma a cikin jihohi 36 na ƙasar da Babban Birnin Tarayya Abuja yana nuna jajircewar shugaban wajen tabbatar da cewa, ya yi duk abin da ya yi alƙawarin zai aiwatar kafin ya bar gadon mulki. Shugaba Buhari ya bayyana hakan ne a ranar Litinin a Abuja a wani taron bita na kwanaki biyu na duba ayyukan Ministoci wanda aka shirya don tantance ci gaban da aka samu don cimma muhimman abubuwan da gwamnatinsa ta sa a gaba,…
Read More