Ra’ayin Manhaja

Zarcewa da ayyukan alheri har bayan Ramadan

Zarcewa da ayyukan alheri har bayan Ramadan

Kamar yau aka fara azumin watan Ramadana ranar 13 ga Afrilu, 2021, wanda ya zo daidai da 1 ga Ramadan, 1442, ga shi a shekaranjiya Laraba, 13 ga Mayu, 2021, wanda ya zo daidai da 30 ga Ramadan, 1442, an kammala azumin, kuma a jiya Alhamis aka gudanar da Sallah Ƙarama, wato ranar 1 ga Shawwal, 1442, kenan. Wannan ya gwada irin izinar da rayuwa ke da ita ta cewa, kullum ran mutum yana ƙarewa cikin hanzari ne. A lokacin da muke yi muku maraba da shigowar watan azumin Ramadana mai taken ‘Yayin da watan Azumi ya }arato’, a shafin…
Read More
Adawa da siyasantar da matsalar tsaro ba za ta fisshe mu ba

Adawa da siyasantar da matsalar tsaro ba za ta fisshe mu ba

A wannan yanayi da mu ke ciki yanzu na taɓarɓarewar tsaro a sassab Nijeriya, jam'iyyun adawa, ƙungiyoyi masu zaman kansu da 'yan ba-ni-na-iya da kuma masu sharhi akan al'amuran yau da kullum a Nijeriya sun taso gwamnati gaba wajen sukar lamirin ta dangane da abinda ya shafi tsaron ƙasar. Yayin da wasu suke kalaman tunzurawa da ɓatanci tare da nuna siyasa ƙarara a cikin kalaman waɗansu. Wanda hakan yake ƙara rura wutar ƙiyayya tsakanin talaka da masu mulkin, talakawa ba sa ganin ƙoƙarin da gwamnati ke yi, har ta kai ga wasu na tunanin yi mata bore. Wasu kuwa suna…
Read More
Tsaro: Gwamnonin Arewa na da rawar takawa

Tsaro: Gwamnonin Arewa na da rawar takawa

Duk da matsayin da jihohin yankin Arewacin Nijeriya suka samu kawunan su a cikin shekaru 16 da su ka shuɗe har zuwa yanzu da gwamnatin APC ke mulkin ƙasar, alamuran yankin suka shiga taɓarɓarewa, harkar tsaron rayuka da dukiyoyin al'umma ya kau, kusan kowane ƙauye su na fama da ruɗani masu garkuwa da mutane, don amsar kuɗin fansa, su na fama da hare-hare da rigingimun makiyaya. Gwamnonin da haƙƙin hakan kuma ya rataya a wuyan su ba su taɓuka ba, don ɗaukar wani mataki, walau na gaggawa ko wanda aka tsara na musamman, don magancewa. Haka nan su na ji,…
Read More
Manufar noma a Arewa: Hannunka mai sanda da gwamnati ke ta yi

Manufar noma a Arewa: Hannunka mai sanda da gwamnati ke ta yi

Tun lokacin zuwan gwamnatin wannan lokaci a shekara ta 2015 ƙarƙashin jagorancin Shugaba Muhammadu Buhari, ta karkata manufar tattalin arzikin Nijeriya kusan kacokan daga ɓangaren ɗanyen mai zuwa kan harkokin noma, inda gwamnatin ta buɗe wuta wajen ingaza dukkan wani sha’ani da yake da alaƙa da fannin noma ta fuskar ɗaukar matakai daban-daban. Gwamnatin Buhari ta samar da shirye-shirye da tsare-tsare kala-kala, domin cimma wannan buri kama daga ƙarfafa samar da rance mai sauƙi ga manoma zuwa ba su tallafin noma. Haka nan gwamnatin ta kuma tabbatar da rufe iyakokin qasar da hana shigo da shinkafa, wanda hakan ya bai…
Read More
Kama muggan makamai a Nijer don safarar su zuwa Maiduguri

Kama muggan makamai a Nijer don safarar su zuwa Maiduguri

A kwanan nan ne jami’an tsaro na Jamhuriyar Nijer suka damƙe wasu muggan makamai da ake yunƙurin shiga da su Nijeriya, don kai su Maiduguri, babban birnin jihar Borno, inda aka fi fama da balahirar yaƙin Boko Haram. Jami’an qasar Nijer ɗin ne suka bayyana hakan, inda suka ce sun kama wata mota ƙirar Toyota Hilux danlare da muggana makaman da suka haɗa da harsashi da bindigogi ƙirar AK-47, inda aka cafke su a Agadez bayan sun tsallako daga kan iyakar Ƙasar Libya da nufin tunkrar Nijeriya, domin kai su. Sashen tsaro na Birnin Agadez da ke Nijer shine ya…
Read More
Yayin da watan Azumi ya ƙarato

Yayin da watan Azumi ya ƙarato

A makon da za mu ne ake sa ran ɗaukar azumin watan Ramadan, wata mai alfarma ga dukkan Musulmin duniya. A ranakun wannan wata, waxanda suke kamawa guda 29 ko 30 a kowacce shekara, Musulmi sukan kaxaita daga aikata wasu muhimman abubuwa a rayuwar ɗan adam da rana, kamar ci, sha da jima’i. Lokacin haramcin hakan yana kamawa ne daga ketowar alfijir zuwa faɗuwar rana a kulliyaumin. To, a zahirin gaskiya ba waɗannan abubuwa ne kaɗai abubuwan da ake sa ran Musulmi ya guje su ba, illa dai kawai za a iya cewa, waɗannan abubuwa guda uku, wato ci, sha…
Read More
Ƙara taɓarɓarewar harkar ilimi a Arewa

Ƙara taɓarɓarewar harkar ilimi a Arewa

Wani rahoton musamman da jaridar Blueprint ta buga a ranar Talata ta makon jiya ya nuna cewa a cikin watanni uku kacal ’yan bindiga sun ci gaba da kai hare-hare a makarantu aƙalla guda biyar a yankunan Arewa-maso-yamma da Arewa-maso-gabas. Hakan ya haifar da damuwa a kan batun samar da ilimi ba kawai a waɗannan yankunan kaɗai ba har ma da lardin Arewa baki ɗayan sa. Rahoton ya ambaci jihohin Katsina, Zamfara da Kaduna a Arewa-maso-yamma da kuma Neja a Arewa-ta-tsakiya a matsayin inda ayyukan ta’addancin ’yan bindigar ya fi ta’azzara. Hari na baya-bayan nan da aka kai, an kai…
Read More
Tashin gwauron zabo da farashi ke yi

Tashin gwauron zabo da farashi ke yi

Rahoton da Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS) ta bayar kwanan nan kan alƙaluman farashin kayan masarufi (CPI) abin damuwa ne matuƙa. Rahoton ya ce jadawalin tashin farashi a Nijeriya ya ƙaru da kashi 12.82 cikin ɗari a watan Yuli da ya gabata, kuma ba a taɓa ganin irin wannan tashin ba a cikin watanni 27 tun daga watan Maris na 2018 lokacin da farashi ya yi bala’in tashi da kashi 13.34 cikin ɗari. Wannan yanayin zai ƙara tavarɓarar da fatara da yunwa da ake ciki, wanda hakan kuma bazarana ce ga Shirye-shiryen Agajin Jama’a (SIPs) waɗanda Gwamnatin Tarayya ke aiwatarwa,…
Read More
Batun dokar hana hadahada da kuɗin kirifto

Batun dokar hana hadahada da kuɗin kirifto

Kwanan nan ne Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya kaɗa hantar wasu ‘yan Nijeriya lokacin da ya tunatar da bankuna da sauran hukumomin da ke kula da hadahadar kuɗi cewa dokar nan da ta haramta amfani da kuɗin intanet, wato kuɗin kirifto (cryto currency), ta na nan daram. Karo na uku kenan a cikin shekara biyar da babban bankin ya yi magana kan harka da irin wannan kuɗi da ake ganin ta na tattare da babban ganganci a cikin ta. Sakamakon hakan, bankuna sun shiga soke duk wani asusu da aka buɗe da sunan yin harka da irin wannan kuɗin. Majalisar…
Read More
Tallafin naira biliyan 600 ga manoma

Tallafin naira biliyan 600 ga manoma

Labarin da aka bayar cewa Gwamnatin Tarayya na shirin bada tallafin sama da naira biliyan 600 don agaza wa manoma abin farin ciki ne. Ba shakka, abin da ya dace ne idan har ana so a faɗaɗa hanyoyin inganta tattalin arzikin ƙasar nan, wanda ya shafe sama da shekara hamsin ya na dogaro da man fetur wajen samun kuɗaɗen shiga. Ministan Aikin Gona Da Raya Yankunan Karkara, Alhaji Sabo Nanono, shi ne ya bayyana labarin a cikin wata sanarwa da Daraktan Yaɗa Labarai na ma’aikatar sa, Mista Theodore Ogaziechi, ya rattaba wa hannu kwanan nan a Abuja. A sanarwar, an…
Read More