06
Aug
Daga NASIR S. GWANGWAZO A ’yan kwanakin nan babu abin da a ke tattaunawa a Arewa da ma Kudancin Nijeriya kamar batun fallasar da ya ke faruwa a Ƙasar Amurka, wanda ya shafi ɗan Nijeriya kuma fitaccen matashin ɗan sanda, wanda ya yi matuƙar suna wajen yaƙi da aikata miyagun laifuka mai muƙamin Mataimakin Kwamishina ’Yan Sandan Nijeriya, wato DCP Abba Kyari. Badaƙalar ta samo asali ne daga binciken da Hukumar Binciken Aikata Miyagun Laifuka ta Amurka, wato FBI, ta gudanar kan fitaccen mai amfani da soshiyal midiya ɗin nan kuma ɗan asalin Nijeriya mazaunin Dubai mai suna Ramon Abbas,…