Wasanni

Man United ta sha alwashin lashe FA Cup bayan ɗaukar Caraboa

Man United ta sha alwashin lashe FA Cup bayan ɗaukar Caraboa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Manchester United ta mayar da hankali kan yadda za ta lashe kofi na biyu a bana, bayan ɗaukar Caraboa Cup da ta yi ranar Lahadi. Karon farko da ƙungiyar Old Trafford ta ɗauki kofi tun bayan cin League Cup da Europa League ƙarƙashin Jose Mourinho a 2016/17. United ta kai zagayen daf da na kusa da na ƙarshe ranar Laraba, bayan da ta ci West Ham United 3-1 a zagaye na biyar a FA Cup a Old Trafford. Kenan United za ta kara da Fulham a quarter finals cikin watan Maris a Old Trafford. Rabon da…
Read More
Girgizar ƙasar Turkiyya: An gano gawar Christian Atsu

Girgizar ƙasar Turkiyya: An gano gawar Christian Atsu

Daga BASHIR ISAH An gano gawar tsohon ɗan wasan ƙwallon ƙafar ƙasar Ghana, Christian Atsu, wanda girgizar ƙasa ta rutsa da shi a Turkiyya. Kafar yaɗa labarai ta Turkiyya ta rawaito cewa, an gano gawar ɗan wasan ne ranar Asabar a ƙarƙashin ɓuraguzan ginin da ya rushe kamar yadda manajansa ya bayyana. Da fari rahotanni sun nuna an ceto marigayin kwana ɗaya da aukuwar iftila'in, amma a ƙarshe ya zamana ba gaskiya ba ne. Sai a ranar Asabar manajan marigayin a Turkiyya, Murat Uzunmehmet, ya shaida wa kafar yaɗa labarai ta DHA cewar an gano gawar marigayin a ƙarƙashin ɓuraguzan…
Read More
Benzema ya kafa tarihin yawan cin ƙwallaye a La Liga

Benzema ya kafa tarihin yawan cin ƙwallaye a La Liga

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Karim Benzema ya kafa tarhin zama na biyu a yawan cin ƙwallaye a gasar La Liga a Real Madrid. Ranar Laraba, Real ta doke Elche 4-0 a wasan mako na 21 a gasar La Liga a Santiago Bernabeu. Marco Asensio ne ya fara cin awallo, sai Karim Benzema ya zura biyu a raga duk a bugun fenariti, sanan Luka Modric ya ƙara na huɗu Benzema ya ci ƙwallo 230 kenan, shine na biyu a yawan ci wa Real Madrid ƙwallaye a La Liga, ya haura Raul mai riƙe da gurbin. Cristiano Ronaldo kyaftin tawagar Portugal shi…
Read More
Rashford ne ɗan wasa mafi cin ƙwallaye tun bayan kammala gasar kofin duniya – Rahoto

Rashford ne ɗan wasa mafi cin ƙwallaye tun bayan kammala gasar kofin duniya – Rahoto

Daga MAHDI M. MUHAMMAD A wani rahoto da Sport Lite ta fitar ya nuna cewa, bayan wasan Manchester United ta tashi 2-2 da Leeds United a kwantan gasar Firimiya ranar Laraba a Old Trafford, cikin waɗanda suka ci wa Man United ƙwallo har da Marcus Rashford, wanda ya zura na 20 a dukkan fafatawa a bana. Haka kuma ɗan ƙwallon tawagar Ingila ya ci na 12 kenan tun bayan da aka kammala gasar kofin duniya a Qatar. Rashford mai shekara 25 ya ci ƙwallo na shida a jere a Old Trafford a Firimiya, bayan Wayne Rooney mai takwas a tsakanin…
Read More
Raphael Varane ya yi ritaya

Raphael Varane ya yi ritaya

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Mai tsaron bayan tawagar ƙwallon ƙafar Faransa da kuma ƙungiyar Manchester United, Raphael Varane, ya sanar da yin ritaya daga buga wa ƙasarsa ƙwallo. Ɗan wasan wanda ya lashe kofin duniya a 2018, ya ci wa Faransa ƙwallaye biyar a wasanni 93 da ya buga tun daga 2013. Wasansa na ƙarshe shi ne wasan ƙarshe na kofin duniya a Qatar 2022, wanda suka yi rashin nasara a hannun Argentina. "Wakiltar ƙasata na tsawon lokaci shi ne babban karamcin da na samu a rayuwata," inji Varane. Ya ƙara da cewa, "a duk lokacin da na saka shuɗiyar…
Read More
Messi na take-taken komawa Barcelona – Rahoto

Messi na take-taken komawa Barcelona – Rahoto

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Wasu na ganin cewa Lionel Messi zai tsawaita kwantiraginsa da ƙungiyar PSG, amma kuma wasu rahotanni na nuna cewa ɗan wasan na Argentina na shirin komawa tsohuwar ƙungiyarsa ta Barcelona. A cewar wani marubucin labarin wasanni na ƙasar Spain Gerard Romero, akwai shakku game da batun tsawaita zaman Messi a PSG. Ya ce, nasarar da ɗan wasan ya samu ta lashe kofin duniya, ta sauya masa tunani musamman yadda yanzu ya daina fifita lamuran wasa akan wasu abubuwa. A ’yan makwannin da suka gabata ne dai aka fara saran ɗan wasan mai shekaru 35 zai cimma…
Read More
An ci tarar Joelinton tare da hana shi tuƙa mota

An ci tarar Joelinton tare da hana shi tuƙa mota

Daga MAHDI M. MUHAMMAD An ci tarar ɗan ƙwallon Newcastle United, Joelington an kuma hana shi tuƙa mota shekara ɗaya, bayan samunsa da laifi tuƙi a cikin mayen barasa. Mai buga wasa daga tsakiyar fili zai biya fam dubu 29, bayan da ya amince da laifin da aka tuhume shi tun farko. 'Yan sanda sun tsare ɗan ƙasar Brazil a lokacin da ya ke tuƙa motarsa ta Marsandi kirar G Wagon ranar 12 ga watan Janairu a Ponteland Road, Newcastle. Bayan da aka yi masa gwajin ko ya sha barasa ne aka same shi da laifin kwankwadar wuce kima da…
Read More
Hada-hadar kasuwar ’yan wasan ƙwallon ƙafa

Hada-hadar kasuwar ’yan wasan ƙwallon ƙafa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Southampton na daf da tabbatar da zaman dindindin na matashin ɗan gaban Senegal Nicolas Jackson, wanda Villarreal ta sa masa farashin yuro miliyan 20. Crystal Palace na son dawo da ɗan wasan tsakiya na Chelsea Conor Gallagher ƙungiyar saboda yadda matashin na tawagar Ingila ya taka rawar-gani a lokacin da yake zaman aro a Eagles ɗin a kakar da ta wuce. Darektan wasanni na Napoli Cristiano Giuntoli ya ce yana da kwarin gwiwa ƙungiyar za ta iya sayen matashin ɗan wasan tsakiya na Angers da Morocco Azzedine Ounahi, wanda kuma ake dangantawa da tafiya Aston Villa…
Read More
AFCON 2025: George Weah ya juya wa Nijeriya baya duk da ziyarar da Osinbajo ya kai ma sa

AFCON 2025: George Weah ya juya wa Nijeriya baya duk da ziyarar da Osinbajo ya kai ma sa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Shugaban Ƙasar Laberiya, George Weah, ya ƙara nuna goyan bayansa ga yunƙurin Makoro na karɓar baƙuncin gasar kofin nahiyar Afirka ta 2025 (AFCON). Tsohon ɗan wasan wanda shi ne ɗan Afirka ɗaya tilo da ya taɓa lashe kyautar gwarzon ɗan ƙwallon ƙafa ta Ballon d’Or, da ake bai wa gwarzon ɗan wasan duniya, ya ce, ya nuna cikakken goyon bayansa ga ƙasar da ta kai wasan kusa da na ƙarshe a gasar kofin duniya na Qatar 2022. Wannan na zuwa ne sa'o'i 72 bayan mataimakin shugaban ƙasa Yemi Osinbajo ya ziyarci ƙasar Laberiya domin halartar wani…
Read More
Aston Villa ta cimma yarjejeniyar ɗaukar Duran

Aston Villa ta cimma yarjejeniyar ɗaukar Duran

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Aston Villa ta cimma yarjejeniyar ɗaukar ɗan ƙwallon tawagar Colombia, Jhon Duran daga Chicago Fire. Duran, mai shekara 19, ya ci ƙwallo takwas ya kuma bayar da shida aka zura a raga a wasa 28 da ya yi wa Chicago. Kammala yarjejeniyar ta alakanta idan an auna koshin lafiyar ɗan wasan, sannan idan ya samu takardar shaidar aiki a Burtaniya. Ɗan ƙwallon zai yi takara a gurbi ɗaya da Ollie Watkins da Danny Ings a ƙungiyar da Unai Emery ke jan ragama, bayan da 'yan wasan biyu suka ci ƙwallo bakwai a tsakaninsu. Duran ya buga…
Read More