17
Jan
Daga BASHIR ISAH Al'umma mazauna Ibadan, babban birnin jihar Oyo, sun shiga firgici da tashin hankali biyo bayan fashewa mai karfi da ta auku da yammacin Talata a birnin. Mazauna yankunan Awolowo, Bodija, Akobo da sauransu sun ce, hatta gidaje da wasu motocin da ke kusa sai da suka amsa sakamakon karfin fashewar. A wani sako da ta wallaffa a shafinta na X, Gwamnatin Jihar Oyo ta ce ta samu rahoton fashewar da ta auku. “Ana kira ga mazauna yankin da su kwantar da hankulansu kasancewar hukumomin tsaro sun sunkuya bincike domin gano musababbin fashewar," in ji Gwamnatin Jihar. Jaridar…
