Editor

9513 Posts
Ɓata-gari sun kai hari asibiti sun yi awon gaba da gawa a Ekiti

Ɓata-gari sun kai hari asibiti sun yi awon gaba da gawa a Ekiti

Daga BASHIR ISAH Wasu bata-garin matasa a Jihar Ekiti sun kai hari Asibitin Koyarwa na Jami'ar Jihar (EKSUTH) da ke Ado-Ekiti, babban birnin jihar inda suka sace wata gawa. MANHAJA ta kalato cewar wannan al’amari ya auku ne a ranar Litinin lamarin da ya haifar da tsaiko a ayyukan asibitin. Bayanai sun ce, gawar da aka sace din ta mahaifin daya daga cikin bata-garin ne. Sai dai, babbu cikakken bayani kan dalilin da ya sa matasan daukar wannan mataki. Faruwar wannan al’amari ya sanya kungiyar likitoci a jihar ta bai wa mambobinta umarnin fara yajin aikin sai-baba-ta-gani domin nuna rashin…
Read More
‘Yan bindiga sun kashe ƙarin mutum 3 daga cikin 10 da suka sace a Abuja

‘Yan bindiga sun kashe ƙarin mutum 3 daga cikin 10 da suka sace a Abuja

*Sun ƙara kuɗin fansa zuwa N700m Daga BASHIR ISAH 'Yan bindigar da suka yi garkuwa da wasu mutum 10 a yankin Dutse, Abuja a ranar 7 ga Janairun da ake ciki, sun kashe karin mutum uku daga cikin mutane 10 da suka yi garkuwa da su. Majiyarmu ta ruwaito cewar, 'yan bindigar sun aikata hakan ne a matsayin gargadi ga 'yan wadanda ke hannunsu kan kudin fansar da suka nema a biya. A cewar majiyar, 'yan bindigar sun kara kudin fansar zuwa Naira miliyan 100 kan kowane mutum sabanin Naira miliyan N60 da suka nema da farko. Da wannan, 'yan…
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu ya isa Owerri don rantsar da Gwamna Hope Uzodinma wa’adi na biyu

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu ya isa Owerri don rantsar da Gwamna Hope Uzodinma wa’adi na biyu

Daga BASHIR ISAH A halin da ake ciki, Shugaban Kasa Bola Tinubu ya isa Owerri, babban birnin Jihar Imo domin shaida bikin rantsar da Gwamna Hope Uzodinma a wa'adin mulkin jihar na biyu. MANHAJA ta kalato cewa, Tinubu ya bar Abuja zuwa Imo ne jim kadan bayan bikin Ranar Tunawa da Sojoji. Bikin rantsarwar na guna ne a babban filin wasannin motsa jiki na Dan Anyiam da ke Owerri. Yayin ziyarar, ana sa ran Shugaba Tinunu zai kaddamar da wasu muhimman ayyuka da gwamnatin jihar ta aiwatar.
Read More
Yadda za ki kula da fatarki a lokacin sanyi (3)

Yadda za ki kula da fatarki a lokacin sanyi (3)

Daga AISHA ASAS A satin da ya gabata, mun kawo yadda za ki iya kula da fatarki, da kuma dabi'un da ya kamata mu dinga yi a lokacin sanyi. A yau za mu tabo wani bangare da ke bukatar kulawa a lokacin sanyi, wato kafa da kuma gashi. A lokacin sanyi ba iya fata ke shiga yanayi ba, asali ma ga wasu kafa ta fi shiga mawuyacin hali fiye da sauran fatar jiki. Kafa wata muhimmiyar vangare ce a jikin mutum da ya kamata a ba ta kulawa ta musamman a lokacin sanyi. Ta yaya za a iya kula da…
Read More
Dole ne a ɗore da ya ƙi da cin hanci da rashawa a Nijeriya

Dole ne a ɗore da ya ƙi da cin hanci da rashawa a Nijeriya

Ranar Alhamis din da ya gabata ne al'ummar duniya suka ware a matsayin ranar yaki da cin hanci da rashawa ta duniya. Majalisar Dinkin Duniya ta kuduri mai lamba 58/4 na ranar 31 ga watan Oktoban shekarar 2003 ta ware ranar na kowace shekara a matsayin ranar wayar da kan jama'a game da laifukan da ke kawo cikas ga cigaba da kuma talauta jama'a. Har ila yau, rana ce ga shugabannin siyasa, gwamnatoci, hukumomin shari'a, kungiyoyin fafutuka da kungiyoyin farar hula don sabunta alkawurran da suka dauka na kawar da wannan abu da aka gano a matsayin wani lamari mai…
Read More
Aminin Pantami ya ba da tallafin N50m don kuɓutar da ‘yan matan da ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su a Abuja

Aminin Pantami ya ba da tallafin N50m don kuɓutar da ‘yan matan da ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su a Abuja

Daga BASHIR ISAH Tsohon Minista kuma fitaccen malamin Islama, Farfesa Isa Pantami, ya sanar cewa an tara kudi Nairia miliyan 50 domin ceto da ‘yan matan zuri’ar Al-Kadriyar da ‘yan binbdiga suka yi garkuwa da su a yankin Abuja. Pantami ya ce wani amininsa ne ya ba da tallafin ragowar Naira miliyan 50 daga cikin miliyan 60 da ‘yan bindigar suka bukaci a biya, bayan da ya tattauna batun da shi. A cewar tsohon ministan, “Alhamdu lil Laah! A kashin kaina ba na goyon bayan biyan kudin fansa ga barayi. Amma tun da a bayyane yake mun rasa ‘yarmu Nabeeha…
Read More
Buni ya samar da romon dimukraɗiyya a Nengere – Hon. Yerima

Buni ya samar da romon dimukraɗiyya a Nengere – Hon. Yerima

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaban Karamar Hukumar Nengere a Jihar Yobe, Hon. Salisu Yerima ya bayyana irin kokarin da Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni ya yi wajen samar da romon dimukradiyya ga al'ummar yankin tun bayan hawansa mulkin jihar a 2019. Hon. Yerima ya ce Gwamna Buni ya yi abin a yaba da irin jagorancinsa na cire kyashi wajen dorawa daga inda tsohon gwamnan jihar, kuma Ministan Harkokin 'Yan Sanda na yanzu, Sanata Ibrahim Geidam ya tsaya. Ya ce an samu nasarori masu tarin yawa da suka haifar wa jihar da mai ido, inda ya ce shirye-shiryen…
Read More
Miyagun ƙwayoyi: Onche ya bukaci al’ummar Nasarawa su hada kai da NDLEA

Miyagun ƙwayoyi: Onche ya bukaci al’ummar Nasarawa su hada kai da NDLEA

Daga JOHN D. WADA a Lafiya Kwamandan hukumar dake yaki da sha tare da safarar miyagun kwayoyi na kasa reshen jihar Nasarawa Peter Onche-Odaudu ya bukaci al’ummar jihar Nasarawa baki daya musamman sarakunan gargajiya su ruka hada kai da hukumar a jihar ta Nasarawa don ci gaba da yaki da masu laifin sha tare da safarar miyagun kwayoyi a jihar da kasa bakidaya. Peter Onche-Odaudu ya yi kiran na musamman ne ta wani sakon sabuwar shekarar 2024 na musamman dauke da sanya hannunsa da aka bai wa wakilinmu kwafi a ofishin hukumar dake birnin Lafiya fadar gwamnatin jihar ranar Talata…
Read More
Yadda Muhammad Rili ya farfaɗo da darajar hukumar KADA a Kaduna

Yadda Muhammad Rili ya farfaɗo da darajar hukumar KADA a Kaduna

Daga SANI SHEHU LERE a Kaduna Sau da yawa mutane kan zabi hukumomin da inda so samu ne a kai su don yin aiki, ba don komai ba, sai don irin maikon da ake hange a cikinsu da saukin aiki. Zuwan Hon. Muhammada Rili Hukumar KADA, ta isa ta canza wa mutane irin wannan tunani, su gane cewa a she kowane ofishi na da irin nasa gwargwadon maikon amma sai in an samu mutumin da ya iya murza gabobin da maikon da zai iya fita. Ma'ana, mutum ke gyara ofis, ba ofis ne ke gyara mutum ba. A kasa da…
Read More
Sheikh Bin Uthman ya amshi muƙamin Hukumar NAHCON a gwamnatin Tinubu

Sheikh Bin Uthman ya amshi muƙamin Hukumar NAHCON a gwamnatin Tinubu

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu ya amince da nadin sabbin mambobin hukumar gudanarwa alhazai ta kasa (NAHCON). A cewar wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasar, Ajuri Ngelale, ya fitar a yammacin ranar Laraba, shugaban kasar, a kudurinsa na ganin an gudanar da ayyukan Hajji na shekarar 2024, ba tare da wata matsala ba, ya nada Jalal Arabi a matsayin shugaban hukumar gudanarwar hukumar. Manhaja ta ruwaito cewa ‘yan makonnin da suka gabata ne Shugaba Tinubu ya nada Arabi a matsayin shugaban riko na hukumar NAHCON. Sabbin mambobin hukumar gudanarwar sun hada…
Read More