03
May
Gwamnatin Faransa na duba yuwuwar yadda za a kawo ƙarshen hare-haren da ke faruwa a tsakanin matasa, bayan cakawa wani ɗan shekara 15 wuƙa da wani matashi ya yi a ƙarshen mako, ɗaya daga cikin jerin hare-haren da ya girgiza al’ummar ƙasar. Firaministan Faransa Gabriel Attal ya shirya tarurrukan da jam'iyyun siyasa kan yadda za a tunkari wannan matsala da ke neman wuce gona da iri. Ƙasar Faransa dai ta fuskanci jerin hare-hare kan matasa daga takwarorinsu a 'yan makonnin nan, inda masu tsatsauran ra'ayi da masu ra'ayin mazan jiya suka danganta wannan matsala da manufofin gwamnati na sassauta sha’anin…
