Editor

9513 Posts
Tudun Biri: Sojoji 12 sun gurfana gaban kotunsu bayan kammala bincike

Tudun Biri: Sojoji 12 sun gurfana gaban kotunsu bayan kammala bincike

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Rundunar Sojojin Nijeriya ta bayyana cewa, ta kammala binciken da aka daɗe ana dakon sakamakonsa kan bom ɗin da aka jefa bisa kuskure kan mutanen ƙauyen Tudun Biri a Ƙaramar Hukumar Igabi da ke Jihar Kaduna. Ta kuma ce, sojojin da aka samu da laifi a kai harin, za su gurfana a gaban kotun soji, domin fuskantar hukunci. Daraktan yaɗa labarai na hedikwatar tsaron Nijeriya, Edward Buba, ne ya bayyana haka a taron manema labaran da aka gudanar a Abuja. A Disambar bara ne wani jirgin sojoji ya jefa bom kan mutanen da ke bikin Maulidi,…
Read More
Makamashi: Mafarki da tabbacin ’yan Nijeriya

Makamashi: Mafarki da tabbacin ’yan Nijeriya

Tare da Bashir Mudi Yakasai Ɗaiɗaikun mutane da ɗaiɗaikun ƙasashe na da mafarke – mafarke na samun abin duniya da suka kira da abubuwa na zahiri da za a iya gani kuma a taɓa kamar makarantu, asibitoci, hanyoyi, gadoji, gidaje wato mahalli har ta kai masana’antu domin samar da ayyukan yi ga miliyoyin ‘yan ƙasa. Ƙasar Kano ita ce ƙasar farko a tarihin mulkin jama’a a dukkan ƙasar Hausa a shekara ta 1770 Miladiyya lokacin mulkin Sarkin Kano Babba Zaki Dan Yaji (1768 – 1776). Muhammadu Babba Zaki ɗan Yaji shine mutum na farko daya gina gidaje masu ɗakuna uku-uku…
Read More
Hada-hadar kasuwar ’yan wasan ƙwallo

Hada-hadar kasuwar ’yan wasan ƙwallo

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ɗan wasan tsakiya na Manchester United da Portugal Bruno Fernandes, mai shekara 29, ya ce makormarsa a Old Trafford ta dogara ne akan ko ƙungiyar ta na son ya cigaba da buga mata wasa har bayan bazara. Newcastle United ba za bada kai ba wajan sayar da dan wasan tsakiya na Brazil Bruno Guimaraes mai shekara 26 kan kuɗi ƙasa da fam miliyan 100 ko rabuwa da ɗan wasa mai kai hari na Sweden Alexander Isak, ɗan shekara 24. Newcastle na son ɗaukar mai tsaron bayan Fulham da Ingila Tosin Adarabioyo mai shekara 26. Adarabioyo, wanda…
Read More
Barcelona ta koma ta biyu a teburin La liga

Barcelona ta koma ta biyu a teburin La liga

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Yayin da ya rage saura wasanni biyar a ƙarƙare La Ligar Sifaniya ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barcelona ta koma matsayi na biyu a teburin gasar da maki 73 bayan da ta tsallake Girona, wacce ke matsayi na uku da 71. Wannan gagarumar nasara da Barcan ta samu na zuwa ne bayan da ta caskala Valencia da ci 4 da 2 a daren ranar Litinin. Kafin tafiya hutun rabin lokaci ƙungiyar Valencia ce ke kan gaba da ƙwallaye 2 da 1. Sai dai bayan dawowa daga hutun rabin lokaci ɗan wasan gaba na Barcelona Robert Lewandowski ya…
Read More
Kotu ta tsare fasto kan aikata fyaɗe

Kotu ta tsare fasto kan aikata fyaɗe

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Wata kotun majistare ta tsare wani limamin coci a gidan yari kan laifin yi wa wata matashiya mai shekaru 22 fyaɗe. Babbar Kotun Majistare da ke Badagry a Jihar Legas ta tisa ƙeyar Fasto Sunday Adewoye zuwa gidan yarin ne a ranar Talaa bayan an gurfanar da shi. Ɗan sanda mai gabatar da ƙarar, Insfekta Ayodele Adeosun, ya shaida wa alqali cewa a ranar 17 ga Afrilu, 2024 ne Fasto Adewoye ya zakke wa matar da ƙarfin tsiya a garin na Badagry. Hakan a cewarsa laifi ne a ƙarƙashin dokar hukunta manyan laifuka ta…
Read More
Iyalai da almajiran Malam Mai Siddi sun yi addu’ar cika shekara 32 da rasuwarsa a Gombe

Iyalai da almajiran Malam Mai Siddi sun yi addu’ar cika shekara 32 da rasuwarsa a Gombe

Ya bada gudunmawa wajen haɗa kan al’umma ta vangaren karatun Ishiriniya Daga ABUBAKAR A BOLARI a Gombe A ranar Juma’ar da ta gabata ne 26 ga watan Afrilu 2024 iyalai da almajiran Sheikh Abubakar Siddi Bolari (Mai Ishiriniya) suka gabatar da addu’o'i na musamman don cika shekara 32 da rasuwarsa. Shi dai Sheikh Malam Abubakar Siddi Mai Ishiriniya Malamin addinin Musulunci ne da ya bada gudunmawa sosai wajen ciyar da addinin Islama gaba, a tsawon rayuwarsa wanda ya bar giɓi mai wuyar cikewa. Tarihin rayuwarsaSheikh Abubakar ɗa ne ga ɗan Abdullahi ɗan Salihu wanda yake jinin sharifai ne da ke…
Read More
Kotu ta haramta wa NERC aiwatar da ƙarin kuɗin wutar lantarkin

Kotu ta haramta wa NERC aiwatar da ƙarin kuɗin wutar lantarkin

Daga BASHIR ISAH Babbar Kotun Tarayya mai zamanta a Kano ta ba bai wa Hukumar Kula da Wutar (NERC) da kamfani Kano Electricity Distribution Company (KEDCO) kan kada su aiwatar da ƙarin kuɗin wutar lantarkin da aka yi ga masu amfani da wutar lantarki na Band A. Kwanankin bayana ne NERC ta umarci kamfanonin rarraba wutar lantarki da su ƙara kuɗin wutar da suke bai wa kostomominsu na rukunin Band A domin samun wadatar wutar lantarki. Sai da daman 'yan Nijeriya sun soki matakin na NERC musamman yadda hukumar ta ɗora da yawan kostomomin nata a tsarin Band A duk…
Read More
Hisbah ta bai wa ‘yan jarida da lauyoyi gurbi a shirin auren zawarawa

Hisbah ta bai wa ‘yan jarida da lauyoyi gurbi a shirin auren zawarawa

Daga BASHIR ISAH Shugaban Hukumar Hisbah na Jihar Kano, Sheikh Aminu Daurawa, ya sanar da bai wa 'yan jarida gurbi guda 50 a shirin auren zawarawan da hukumar za ta yi nan gaba. Daurawa ya bayyana haka ne a wata hira da ya yi da manema labarai ranar Laraba a Kano. Ya ce, sako 'yan jarida da sauransu a cikin shiri, zai taimaka wajen daɗa bunƙasa shi. Daurawa ya ƙara da cewa, shirinta na gaba zai haɗa har da lauyoyi da ma'aikatan kiwon lafiya da sauransu. Wannan na zuwa ne bayan da hukumar ta samu nasarar ƙulla aure 1,800 a…
Read More
Sarkin Kano ya buƙaci a dawo da Makarantar Sojojin Sama ta Kano

Sarkin Kano ya buƙaci a dawo da Makarantar Sojojin Sama ta Kano

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Mai Martaba Sarkin Kano, Alh Aminu Ado Bayaro, ya yi kira ga Shugaban sojojin sama na Nijeriya kan ya yi ƙoƙari wajen dawo da Makarantar Sojojin sama da ke garin Kwa a yanki Ƙaramar Hukumar Dawakin Tofa wadda aka rufe sakamakon rashin tsaro a watannin baya. Basaraken ya yi wannan kira ne lolacin da Shugaban Sojojin Sama na Nijeriya, Hassan Bala Abubakar, ya ziyarce shi a fadarsa a ranar Alhamis. Ta cikin wata sanarwa da sakataren yaɗa labarai na Masarautar Kano, Abubakar Balarabe Kofar Na'isa, ya tura wa Blueprint Manhaja ya ce, Sarkin ya ƙara…
Read More
Ranar Ma’aikata: Ƙarin albashi da kashi 35 ɓata lokaci ne — NLC

Ranar Ma’aikata: Ƙarin albashi da kashi 35 ɓata lokaci ne — NLC

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Ƙungiyar Ƙwadago ta Nijeriya (NLC) ta yi watsi da ƙarin albashin da Gwamnatin Tarayya ta yi musu a matsayin “vata lokaci.” Manhaja ta ruwaito a daren Talata cewa gwamnatin ta yi wa ma’aikatanta ƙarin kashi 25 zuwa 35 na albashinsu; ’yan fansho kuma kashi 20 zuwa kashi 28. Sanarwar da mai magana da yawun hukumar kula da albashi ta ƙasa (NSIWC), Emmanuel Njoku, ya fitar ta duk ƙarin za su fara aiki ne daga watan Janairun 2024. Njoku ya kuma shaida wa Manhaja cewa za a biya ma’aikatan cikon ƙarin albashin na watannin da…
Read More