Editor

9513 Posts
Wanne darasi karatun littattafai ke koyarwa?

Wanne darasi karatun littattafai ke koyarwa?

Tare da ABBA ABUBAKAR YAKUBU Littafi abu ne mai muhimmanci ga rayuwar ɗan adam, duba da yadda littafi ke taimakawa wajen adana muhimman bayanai da labarai da suka jiɓanci harkokin rayuwa daban-daban, kama daga tarihi, bayanan da suka shafi harkokin kimiyya da fasaha da tattalin arziki, tarihin ƙasa da muhimman mutane da al'adu da sauransu. Ranar littafi da kare 'yancin mallakar fasaha ta duniya ta samo asali ne tun a shekarar 1616 lokacin da aka yi rashin wasu fitattun marubuta irinsu Cervants, da Sharkspare da Inca Garcilaso de La vega. Kana a shekarar ce kuma aka samu wanzuwar wasu fitattun…
Read More
Ranar Ma’aikata: Gwamnati ta ayyana 1 ga Mayu, ranar hutu ga ma’aikata

Ranar Ma’aikata: Gwamnati ta ayyana 1 ga Mayu, ranar hutu ga ma’aikata

Daga BASHIR ISAH Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranar Laraba, 1 ga watan Mayu, a matsayin ranar hutun gama-gari albarkacin Bikin Ranar Ma'aikata na bana. Bayanin hakan na ƙunshe ne cikin sanarwar da Babban Sakataren Ma'aikatar Cikin Gida, Dr Aishetu Ndayako, ta fitar ranar Talata a Abuja. Aishetu ta ce, Ministan Harkokin Cikin Gida, Dr Olubunmi Tunji-Ojo ne ya ayyana ranar hutun a madadin Gwamnatin Tarayya. Tunji-Ojo ya jaddada buƙatar aiki da ƙwazo a ɗaukacin ɓangarorin ƙwadago, kana ya ƙara haskaka ƙudurin gwamnatin Shugaba Bola Tinubu na ƙoƙarin samar da walwala ha ma'aika da kuma son ganin ma'aikata sun zamo masu…
Read More
Ta ya za ku iya ƙara wa ƙwaƙwalwarku kaifi?

Ta ya za ku iya ƙara wa ƙwaƙwalwarku kaifi?

Daga AISHA ASAS Mai karatu barkanmu da sake kasancewa tare. A wannan makon shafin kwalliya na jaridar Blueprint Manhaja zai yi duba ne kan muhimmin abu da lafiyar jikinmu ke buƙata ko in ce jiki ke buƙata don tabbatar da gudanar da ayyukan yau da kullum ba tare da matsala ba. Ba komai nake magana kai ba face kaifin ƙwaƙwalwa. Ƙwaƙwalwar ɗan adam wata halitta ce mai cike da abin ban mamaki, kuma muhimmancinta ga jikin mutum lamari ne mai gima. Duba da cewa kusan kowacce gava ta jikin ɗan adam tana da hedikwata a ƙwaƙwalwa, wadda daga can ne…
Read More
Za mu gurgunta samar da fetur muddin ba a biya mu bashin N200bn ba — IPMAN

Za mu gurgunta samar da fetur muddin ba a biya mu bashin N200bn ba — IPMAN

Daga BASHIR ISAH Ƙungiyar Masu Dakon Fetur ta Nijeriya (IPMAN), ta yi barazanar gurgunta samar da fetur afaɗin ƙasa muddin ba a biya ta bashin Naira biliyan 200 da take bi ba. Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ƙarancin fetur ke ci gaba da ta'azzara lamarin da ya yi sanadiyar ƙarin farashin fetur a sassan ƙasa, inda a yanzu ake sayar da fetur tsakanin N610 da N800 kan lita guda a wasu wurare, sannan N1000 zuwa N1200 a kasuwar bayan fage. Jigo a IPMAN, Mazi Oliver Okolo ne ya yi wannan barazanar, kuma cewa da goyon bayan shugabancin…
Read More
Emefiele ba ya bayar da kwangila sai da cin hanci, in ji shaida

Emefiele ba ya bayar da kwangila sai da cin hanci, in ji shaida

Daga BASHIR ISAH Mutum na biyu da ke ba da shaida a kan shari'ar da tsohon Gwamnan CBN, Godwin Emefiele ke fuskanta, ya bayyana wa Kotu ƙarara cewa lallai Emefiele ba ya ba da kwangila ba tare da ya karɓi cin hanci ba. John Ayo wanda ya kasance tsohon Darakta na Sashen Labarai na CBN, ya bayyana haka ne ga Babban Kotun da ke zamanta a Ikeja, Jihar Legas. Ya bayyana haka ne a lokacin da yake ba da shaida a gaban Alƙali Rahman Oshodi yayin zaman da kotun ta yi a ranar Litinin. Emefiele na fuskantar shari'a ne kan…
Read More
Ba zan iya auren duk wanda ba ya son harkar fim ba – Asmee Wakeel

Ba zan iya auren duk wanda ba ya son harkar fim ba – Asmee Wakeel

Daga MUKHTAR YAKUBU  A wani saƙo da ta saki mai kama da mayar da martani, Jaruma a masna'antar finafinan Hausa ta Kannywood, Asmau Wakili wadda aka fi sani da Asmee Wakili, ta bayyana cewar ita sam ba za ta iya zama da duk wanda ba ya son sana’arta ta fim da take yi ba. Jaruma Asmee Wakeel ta bayyana hakan ne a cikin wani bidiyo da ta wallafa a shafinta na TikTok, wanda hakan ya sa ake ganin mayar da martani ne ga mutanen da suke kyamatar auren 'yan fim tare da jifan su da kalamai marassa daɗi a game…
Read More
Rasuwar wacce nake so ce sanadin fara waƙa ta – Halifa Maiyabo 

Rasuwar wacce nake so ce sanadin fara waƙa ta – Halifa Maiyabo 

Daga IBRAHIM HAMISU  Ahmad M. Ahmad da a ka fi sani da Halifa Maiyabo matashin mawaƙi ne, wanda ya ke tasowa a duniyar waƙoƙi. A tattaunawarsa da Wakilin Blueprint Manhaja, IBRAHIM HAMISU, a Kano za ku ji taƙaitaccen tarihin rayuwarsa da kuma yadda a ka yi ya samu kansa a harkar waƙa. A sha karatu lafiya: MANHAJA: Ka gabatar mana da kanka? HANIFA MAIYABO: Sunana Ahmad M. Ahmad amma an fi sani na da Halifa Maiyabo. Ba mu taƙaitaccen tarihinka? An haife ni a sabon titi na Dandago cikin birnin Kano, daga bisani yanayi na rayuwa ya sa mu ka…
Read More
An gano gawar budurwar da aka sanar da ɓacewarta a Abuja

An gano gawar budurwar da aka sanar da ɓacewarta a Abuja

Daga BASHIR ISAH An gano gawar Murjanatu Zubaiaru bayan da 'yan uwanta suka ba da sanarwar ɓacewarta a Abuja. Kafin mutuwarta, Murjanatu ɗaliba ce 'yar aji huɗu a Jami'ar Abuja. A cewar kawun marigayiyar, Alhaji Zubairu Jibrin Yewuti kuma tsohon Mataimakin Shugaban Hukumar Kwali, a ranar Juma'ar da ta gabata Murjanatu ta bar gida zuwa makaranta amma ba a ga dawowarta ba, kuma wayarta ba ta shiga. Ya ce, "Iyayenta sun tuntuɓe ni kan ko na ga Murjanatu alhali ba ta zo gidana ba kamar yadda aka yi zato. Duk ƙoƙarin da muka yi don ji daga gare ta waya,…
Read More
Yanzu-yanzu: JAMB ta saki sakamakon UTME na 2024

Yanzu-yanzu: JAMB ta saki sakamakon UTME na 2024

Daga BASHIR ISAH Hukumar Shirya Jarrabawar Neman Gurbin Karatu a Manyan Makarantu (JAMB), ta saki sakamakon jarrabawar da ta shirya ta 2024. Shugaban JAMB, Fargesa Ishaq Oloyede ne ya sanar da hakan ga manema labarai alran Litinin a hedikwarar hukumar da ke yankin Bwari, Abuja.
Read More