Editor

9513 Posts
Gwamnatin Zamfara ta tantace tsoffin ma’aikata 3079, ta biya bashin giraduti na N2.3bn

Gwamnatin Zamfara ta tantace tsoffin ma’aikata 3079, ta biya bashin giraduti na N2.3bn

Daga BASHIR ISAH Gwamnatin Jihar Zamfara ta bayyana cewa ta samu nasarar tantance ma'aikatan jihar da suka yi ritaya 3,079 a ƙoƙarin da take yi na ganin ta warware bashin giradutin da ake bin gwamnatocin da suka gabata. Rabon tsoffin ma'aikatan jihar da samun haƙƙinsu na giraduti tun a shekarar 2011, kamar yadda sanarwar manema labarai mai ɗauke da sa hannun Kakakin Gwamna, Sulaiman Bala Idris ta nuna. Sulaiman ya ce kawo yanzu an biya masu karɓar fansho a matakin jiha da ƙananan hukumomi su 1746 kuɗi N2,312,841,065.08. Ya ce a Juma'ar da ta gabata aka fara biyan kashi na…
Read More
An sulhunta tsakanin Gwamna Abba da Sheikh Daurawa

An sulhunta tsakanin Gwamna Abba da Sheikh Daurawa

*Daurawa ya amince ya koma muƙaminsa na shugabancin Hisbah Daga BASHIR ISAH Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya amince ya koma kan muƙaminsa a matsayin Kwamandan Hukumar Hisbah domin ci gaba daga inda ya tsaya. Daurawa ya amince da hakan ne bayan da malamai suka shiga suka suhulta tsakaninsu da Gwamnan Kano, Abba Kabir. Tun farko, Malam Daura ya sanar da ajiye muƙamin nasa cikin wani faifain bidiyo da aka yaɗa inda aka ji shi yana bai wa Gwamna Kabir haƙuri kana daga bisani ya ce ya ajiye shugabancin Hisbah. Gwamna Kabir ya yi ƙorafi kan yadda hukumar ta Hisbah ke…
Read More
Ramadan: ‘Ku sassauta farashin kayan abinci’ — kiran Sarkin Kano, Ado-Bayero ga ‘yan kasuwa

Ramadan: ‘Ku sassauta farashin kayan abinci’ — kiran Sarkin Kano, Ado-Bayero ga ‘yan kasuwa

Daga BASHIR ISAH Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado-Bayero, ya yi kira ga 'yan kasuwa da su sauke farashin kayan abinci da sauransu domin bai wa al'umma damar yin azumin Ramadan cikin walwala. Basaraken ya yi wannan kira ne a wajen taron ƙaddamar da littafi mai taken: “Dauloli a Ƙasar Hausa” wallafar Farfesa Sa’idu-Mohammed Gusau wanda ya gudana ranar Lahadi a Zaria. Kazalika, ya yi kira ga masu hannu da shuni da su dubi Allah su taimaka wa mabuƙata yayin watan na Ramadan. Ado Bayero ya yaba wa marubucin littafin bisa ƙoƙarin da ya yi wajen bayyana Masarautun Hausa da ke…
Read More
Dattawan Arewa sun yi gargaɗi kan shirin kwashe jiragen yaƙi daga Zaria zuwa Legas

Dattawan Arewa sun yi gargaɗi kan shirin kwashe jiragen yaƙi daga Zaria zuwa Legas

Daga BASHIR ISAH Ƙungiyar Dattawan Arewa, NEF, ta yi gargaɗin shirin da ake zargin ana yi na kwashe wasu jiragen yaƙi daga Kwalejin Koyon Tuƙin Jirgin Sama, NCAT, da ke Zaria a Jihar Kaduna zuwa Jihar Legas. Sanarwar da ta fitar ranar Lahadi ta hannun Daraktan Hulɗa da Jama'a, Abdul-Azeez Suleiman, ƙungiyar ta ce jita-jitar da ake yaɗawa abin damuwa ne ainun musamman idan aka yi la'akari da daɗaɗɗen tarihin cibiyar da kuma rawar da take takawa ga cigaban fannin sufurin jiragen saman ƙasar nan. Ƙungiyar ta yi ra'ayin "sake ma jiragen wuri na da mummunan sakamako ba ga cibiyar…
Read More
Hatta ƙanzo ma ya yi tsada

Hatta ƙanzo ma ya yi tsada

Tare da NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Ɗan Nijeriya ba ya buƙatar wani zurfin ilimi wajen fahimtar yanda tattalin arzikin Nijeriya da ma wasu hasashen duniya ya samu koma baya. Ƙasashen ba sai can wata nahiyar ba daga ma makwabta za a iya fahimtar yadda rayuwa ta yi tsada. Mun duba yadda gabanin janye takunkumin ECOWAS kan jamhuriyar Nijar a ka samu matsala gwamnatin Niamey da talakawa ke ta kuka har ta kai ga shigar da kara kotun ECOWAS a Abuja. Mu tuna yadda rufe iyakokin Nijeriya na ƙasa zamanin tsohuwar gwamnatin Buhari ya jawo tsadar kayan abinci musamman shinkafa duk da…
Read More
Tsadar Rayuwa: ‘Abin da muka shuka muke girba’ – Shettima

Tsadar Rayuwa: ‘Abin da muka shuka muke girba’ – Shettima

Daga BASHIR ISAH Matamakin shugaban Ƙasa Kashim Shettima, ya bayyana cewa abin da aka shuka a baya shi ake girba a yanzu dangane da tsadar rayuwar da ake fuskanta a ƙasa. Shettima ya buƙaci ‘yan Nijeriya da a kula da yadda suke bayyana fushinsu game da matsalolin tattalin arzikin da ƙasa ke fama da su a wannan hali. Ya ce dukkanin abubuwan da ake gani a yanzu sakamakon abubuwan da aka aikata a gwamnatocin a baya ne wanda ƙasar ke ƙoƙarin daidaita komai don inganta tattalin arzikin ƙasa. Ya ci gaba da cewa, kamar kowace gwamnati, ita gwamnatin Shugaba Bola…
Read More
An samu ɓullar cutar ƙyanda a Kano – Hukuma

An samu ɓullar cutar ƙyanda a Kano – Hukuma

Daga BASHIR ISAH Hukumomi a yankin Ƙaramar Hukuma Kano Municipal sun tabbatar da ɓullar cutar ƙyanda a wasu sassan yankin. Kodinetan Hukumar Kula da Lafiya a Matakin Farko na yankin, Alhaji Aliyu Jinjiri Kiru, shi ne ya bayyana haka yayin taro da kwamitin bada agajin gaggawa da suga shirya a sakatariyar hukumar a ranar Asabar da ta gabata. Cikin sanarwar da ta fitar, Jami'ar Yaɗa Labarai ta yankin, Fatima Abdullahi, ta naƙalto Kodinetan ya ce, sun samu rahoto daga cibiyoyin kula da lafiya a sassan yankin game da ɓullar cutar ƙyada da sauran cututtuka. Jami'in ya ƙara da cewa, wuraren…
Read More
‘Rumbun kayan abincin da aka wawashe ba namu ba ne’ — NEMA

‘Rumbun kayan abincin da aka wawashe ba namu ba ne’ — NEMA

Daga BASHIR ISAH Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta ƙaryata rahotannin da suka ce rumbun kayan abincin da ɓatagari suka wawashe ranar Lahadi a yankin Abuja mallakarta ne. Mai magana da ywun NEMA, Manzo Ezekiel ne ya bayyana haka a cikin sanarwar da ya fitar a ranar Lahadi. A ranar Lahadi wasu ɓatagari suka fasa rumbun kayan abinci mallakar Sashen Harkokin Noma na Hukumar FCT tare da wawashe kayayyakin da ke adane cikinsa. Wani jami'in sashen, Zakari Aliyu, shi ne ya tabbatar wa tashar Channels Television hakan ta saƙon SMS da ya aike mata cewa rumbun mallakar sashen…
Read More
Yadda aka yi wa ’yan canji rusau a Abuja

Yadda aka yi wa ’yan canji rusau a Abuja

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Hukumar Babban Birnin Tarayya ta yi rusau a babbar cibiyar hada-hadar ’yan canji da ke Unguwar Zone 4 da ke Abuja. An rusa rumfunan wucin gadi da bacoci tare da sare bishiyoyi a yayin aikin rusau ɗin da aka gudanar ranar Laraba. Daraktan Sashen Kula da Gine-gine na hukumar, Mukhtar Galadima, wanda ya jagoranci aikin, ya bayyana wa ’yan jarida cewa ɓata-gari suna amfani bacocin da rumfunan wucin gadin da ke wurin a matsayin maɓoyarsu a birnin. Mukhtar Galadima ya ƙara da cewa wurin ya zama cibiyar masu aikata manyan laifuka, wanda hakan barazana…
Read More
‘Duk jam’ina da ya nemi cin hanci ku sanar da ni’ Tinubu ga ‘yan kasuwar Qatar

‘Duk jam’ina da ya nemi cin hanci ku sanar da ni’ Tinubu ga ‘yan kasuwar Qatar

Daga BASHIR ISAH Shugaba Bola Tinubu ya yi kira ga 'yan kasuwa na ƙasa da ƙasa kan cewa kada su bai kowa cin hanci kafin gudanar da harkokinsu a Nijeriya, kuma duk wani jami'insa da ya nemi a ba shi cin hancin a kai ƙararsa. Tinubu ya bayyana haka ne sa'ilin da yake jawabi a wajen taron Zuba Jarida na Nigeria-Qatar ranar Lahadi a Doha, Qatar. A cewarsa, “Kada ku bai wa kowa cin hanci, kuma duk wanda ya karɓa ko ya nemi ku ba shi cin hanci, ku sanar da mu." Shugaban ya ƙara da cewa a shirye Nijeriya…
Read More