03
Mar
Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaba Bola Tinubu ya tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa gwamnatinsa za ta sake fasalin ƙasar kamar yadda ya yi alƙawari tun da farko, amma ya lura cewa dole ne a aza harsashi mai kyau. Tinubu ya bayar da wannan tabbacin ne a wata ziyarar da ya kai wa jagoran ƙungiyar siyasa da zamantakewar al’ummar Yarabawa ta ƙasa, Afenifere, Pa Reuben Fasoranti, a Akure, Jihar Ondo ranar Laraba. Bayan ganawar sirri da wasu zaɓaɓɓun shugabannin ƙungiyar, sakataren yaɗa labaran ƙungiyar na kasa, Mista Jare Ajayi, ya ruwaito shugaban qasar na tabbatarwa ‘yan Nijeriya cewa zai…
