ukarofi

11686 Posts
Matsalar hare-haren ‘yan bindiga ta ragu sosai a lokacin Raɗɗa – Joɓe

Matsalar hare-haren ‘yan bindiga ta ragu sosai a lokacin Raɗɗa – Joɓe

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Mataimakin gwamnan jihar Katsina, Faruk Joɓe, ya ce a lokacin da gwamnatin Dikko Radda ta kama aiki a shekarar 2023, hare-haren ‘yan bindiga da sauran matsalolin tsaro sun yi ƙamari a kusan ƙananan hukumomi 26 daga cikin 34 na jihar. Jobe ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis yayin da yake wakiltar gwamna Radda a taron rubu’i na biyu na shekarar 2026 na daraktocin hukumomin tsaro na jihohin Arewa maso Yamma wanda aka gudanar a shalkwatar hukumar tsaro ta farin kaya (SSS) da ke Katsina. Taron, mai taken “Haɗa Kai Don Yaƙar Ta’addanci”, ya…
Read More
Tsadar kayan masarufi ta ƙaru a watan Yuli

Tsadar kayan masarufi ta ƙaru a watan Yuli

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Farashin kayayyakin masarufi ya ƙaru a watan Yuli a Nijeriya, duk da matakan da Gwamnatin Tarayya ta ɗauka domin bunƙasa samar da kayayyaki a cikin gida da rage kuɗin sarrafa su, da nufin sauƙaƙa wa ’yan ƙasa halin tsadar kayan abinci. Hauhawar farashin ta haifar da damuwa game da tasirin matakan da gwamnati ke ɗauka domin samar da sauƙi a farashin kayan abinci. Sabbin alƙaluman da Hukumar ƙididdiga ta ƙasa (NBS) ta fitar sun nuna cewa farashin kayan abinci ya ƙaru da kashi 20.31 cikin 100 cikin watanni 12 da suka gabata. Rahoton ya…
Read More
Ya kamata gwamnatin Kano ta sake tunani kan shiga kasuwancin sufurin jiragen sama — Abbati Baƙo

Ya kamata gwamnatin Kano ta sake tunani kan shiga kasuwancin sufurin jiragen sama — Abbati Baƙo

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano Masanin kimiyyar siyasa da tattalin arziki, Abbati Baƙo, ya yi kira ga Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, da ya sake duba shirin kafa kamfanin jirgin saman da gwamnatin jihar za ta mallaka. Abbati Baƙo ya yi wannan kiran ne a cikin wata buɗaɗɗiyar wasiƙa da ya aikewa Gwamnan Kano, inda ya bayyana cewa jihar na buƙatar mayar da hankali kan muhimman abubuwan more rayuwa da jin daɗin al’umma, maimakon gwamnati ta shiga harkar gudanar da kasuwancin sufurin jiragen sama. Ya ce Kano za ta iya samun ci gaba sosai, amma ya kamata ta…
Read More
Kwastom ta miƙa bindiga 399 da aka ƙwace ga ofishin Ribadu

Kwastom ta miƙa bindiga 399 da aka ƙwace ga ofishin Ribadu

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Hukumar Kwastom ta Nijeriya ta miƙa bindiga guda 399 da aka ƙwace tare da tarin wasu muhimman kayayyakin bindigogi, ga Ofishin Mai Bai wa Shugaban ƙasa Shawara Kan Harkokin Tsaro, Malam Nuhu Ribadu, bayan kammala bincike kan wani katafaren makaman da aka tare a tashar jiragen ruwa ta Tsibirin Tincan da ke Legas. Shugaban Hukumar Kwastom ta Nijeriya, Adewale Adeniyi, ne ya bayyana hakan a ranar Litinin, inda ya ce an kammala haɗa bindigogin da aka tarwatsa tare da gudanar da cikakken bincike kan kayayyakin da aka kama. A cewarsa, binciken ya tabbatar da cewa kayan…
Read More
Kotu ta umarci bankuna 71 su rufe asusun da aka ajiye kuɗaɗen damfarar bankin Access

Kotu ta umarci bankuna 71 su rufe asusun da aka ajiye kuɗaɗen damfarar bankin Access

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Kotun Tarayya da ke zama a Legas ta umarci bankuna da sauran cibiyoyin hada-hadar kuɗi guda 71 da su sanya takunkumin fitar da kuɗi daga wasu asusu da ake zargin an yi amfani da su wajen adana wani kaso na Naira biliyan 1.34 da aka karkatar ba bisa ƙa’ida ba daga asusun wasu kwastomomin Bankin Access, ta hanyar manhajar bankin ta intanet mai suna Access SME App. Mai shari’a Akintayo Aluko ne ya bayar da umarnin a ranar Litinin, bayan lauyan Bankin Access, Ifeoma E. Enyinnaya, ta shigar da buƙatar gaggawa a gaban kotun ba tare…
Read More
Majalisar NSDC ta jawo jarin Dala biliyan ɗaya don Nijeriya ta daina dogaro da sukarin waje

Majalisar NSDC ta jawo jarin Dala biliyan ɗaya don Nijeriya ta daina dogaro da sukarin waje

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Majalisar Bunƙasa Masana’antar Sukari ta ƙasa (NSDC) ta ƙara ƙaimi wajen jawo jarin masana’antar sukari, inda ta ƙulla haɗin gwiwar zuba jari na Dala biliyan 1 da kamfanin SINOMACH na ƙasar Chana, domin hanzarta samar da sukari a cikin gida da rage dogaro da shigo da shi daga ƙasashen waje. Haɗin gwiwar na daga cikin shirin Asusun Hanzarta Ayyukan Sukari na Naira biliyan 10, wanda NSDC ta kafa tare da Bankin Masana’antu a ƙarƙashin Shirin Haɗa Samar da Kayayyaki a Cikin Gida (BIP). Babban Sakatare kuma Babban Daraktan NSDC, Kamar Bakrin, ne ya bayyana hakan a…
Read More
Majalisar Dokokin Nijeriya ce majalisa mafi yawan ma’aikata a duniya — Magatakarda

Majalisar Dokokin Nijeriya ce majalisa mafi yawan ma’aikata a duniya — Magatakarda

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Majalisar Dokokin Tarayyar Nijeriya na da ma’aikata sama da 14,000, ban da ’yan majalisar tarayya 469 da kuma ɗimbin baƙi da ke ziyartar majalisar, lamarin da ya sanya ta zama ɗaya daga cikin majalisun da suka fi yawan ayyuka a duniya. Magatakardar Majalisar Dokokin Nijeriya (CNA), Kamoru Ogunlana, ne ya bayyana hakan a ranar Talata yayin taron ƙarshe na shirin ƙara wa mataimakan ’yan majalisa ƙwarewa a Majalisa ta 10. Ogunlana ya ce, yawan ma’aikatan majalisar, ’yan majalisa da kuma baain da ke ziyartar majalisar a kullum ya sa gudanar da ayyukan majalisar tarayya ya kasance…
Read More
AI zai taimaka wa ƙanana ’yan kasuwa rage kashe kuɗaɗe – Bincike

AI zai taimaka wa ƙanana ’yan kasuwa rage kashe kuɗaɗe – Bincike

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Wani sabon bincike ya nuna cewa amfani da ƙirƙirarriyar basira ta AI na iya taimaka wa ƙananan da matsakaitan ’yan kasuwa a Nijeriya wajen inganta aiki, rage kashe kuɗaɗen gudanarwa da kuma ƙara musu damar gogayya a kasuwa. Binciken, wanda Dr Ayodeji Idowu ya gudanar kuma aka wallafa a International Journal of Comparative Studies in International Relations and Development, ya ce ci gaban fasahar ajiyar bayanai a ma'adana, wato cloud computing, dandamalin zamani masu sauƙin amfani da kuma API ya rage wahalar da ƙananan kamfanoni ke fuskanta wajen rungumar fasahar AI. Masanin ya bayyana cewa ƙananan…
Read More
Sarrafa amfanin gona a gida ne ginshiƙin wadatar abinci a Nijeriya – Tajudeen

Sarrafa amfanin gona a gida ne ginshiƙin wadatar abinci a Nijeriya – Tajudeen

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Kakakin Majalisar Wakilan Tarayyar Nijeriya, Hon. Abbas Tajudeen, ya sake jaddada aniyar Majalisar Dokokin Tarayya na samar da cikakken goyon baya da kariya ga ’yan kasuwa da masu zuba jari na cikin gida da ke taka muhimmiyar rawa wajen bunƙasa masana’antu da samar da kayayyaki a Nijeriya. Kakakin ya bayyana hakan ne a ranar Asabar yayin bikin ƙaddamar da sabuwar masana’antar Simkay Foods Limited da za ta riƙa sarrafa masara tare da samar da garin masara da kuma abubuwan da suka shafi masara na masara a yankin Zazzau Industrial Park and Industries (ZIPI) da ke Zariya,…
Read More
Naira ta ƙara ƙarfi yayin da asusun waje ya haura Dala biliyan 52.5 — CBN

Naira ta ƙara ƙarfi yayin da asusun waje ya haura Dala biliyan 52.5 — CBN

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Kimar Naira na ci gaba da samun tagomashi, yayin da tazarar farashinta tsakanin kasuwar hukuma da ’yan canjin kuɗi ta ragu zuwa ƙasa da kashi biyu cikin 100. A halin da ake ciki, Asusun Ajiyar ƙasar Waje na Nijeriya ya haura dala biliyan 52.5 zuwa ranar 17 ga Yuli, 2026, matakin da ya kai mafi girma cikin shekaru 17, tare da zarce burin shekara-shekara da Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya sanya. CBN ya ce, wannan ƙaruwa ta samu ne sakamakon ci gaba da shigowar kuɗaɗen waje cikin ƙasar da kuma sake farfaɗowar amincewar masu zuba jari…
Read More