02
Feb
Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Kakakin Majalisar Tarayya, Abbas Tajuddeen ya bayyana a ranar Talata cewa Majalisar Tarayya za ta yi taro na musamman dangane da gagarimar matsalar tsaron da ta addabi Nijeriya baki daya. Ya bayyana haka yayin da aka koma zaman majalisa, inda ya ke cewa matsalar tsaro a kasar nan ta yi muni kuma ta kazanta matukar gaske. “Ina bada shawarar gudanar da Taron Majalisar Tarayya kan Matsalar Tsaro. Taron zai kasance ya zama wurin da za a bijiro da shawarwari daga bakin masu ruwa da tsaki a bangarori da dama, kamar jami’an tsaro, sarakunan gargajiya,…
