17
Feb
Daga BASHIR ISAH Gwamnatin Tarayya ƙarƙashin jagorancin Bola Ahmed Tinubu, ta kira taron gaggawa tare da kamfanoni masu samar da siminti domin tattauna tashin farashin siminti a ƙasa. Kafar Nairametrics ta rawaito cewa, a halin yanzu farashin buhun siminti mai nauyin 50kg a sassan Legas ya kai N9,500. Majiyar ta ƙara da cewa a watan Janairun da ya gabata, farashin buhun simintin bai wuce N6,000 zuwa N6,500 a nan Legas ɗin ba. Tuni dai wasu ƙananan ‘yan kasuwa suka daina sayar da siminti don gudun abin da ka je ya dawo na hauhawar farashinsa. Sai dai a matsayin wani mataki…
