Kasuwanci

Zanga-zanga: Farashin kaya ya tashi a Kano, kasuwar karuwai ta faɗi

Zanga-zanga: Farashin kaya ya tashi a Kano, kasuwar karuwai ta faɗi

Bayan shafe kwanaki ana zanga-zanga a faɗin ƙasa, abubuwa sun tsaya da dama a ƙasar musamman al'amuran kasuwanci. Zanga-zangar yunwar a na sa rai za a ƙare ta 10 ga watan Agusta 2024. Zanga-zangar da ta fara a mastayin ta lumana ta canza salo ta koma rikici musamman a garuruwan Kano da Kaduna. A Kaduna, bankuna da kasuwancin ya fara dawowa dai dai bayan rage dokar hana zirga-zirga da aka sanya a Kaduna da Zaria. Kasuwar Central Market ta Kaduna ta samu masu siyayya sun fito da dama domin sayen kayan abinci da sauran kayan masarufi. A Kano kuwa, nan…
Read More
Shugabar ƙasar Bangladesh Sheik Hasina ta gudu bayan masu zanga-zanga sun afka fadarta

Shugabar ƙasar Bangladesh Sheik Hasina ta gudu bayan masu zanga-zanga sun afka fadarta

Shugabar ƙasar Bangladesh ta arce bayan da masu zanga-zanga su ka afka fadar ta. Faifan bidiyo da ke yawo ya nuna yadda masu zanga-zangar su ka kutsa cikin fadar suna ta ɗaukar abubuwan da suke so. Shugabar wadda ta jima ta na mulki ance ta hau wani jirgin soja ta arce bayan da masu zanga-zanga suka ƙi bin dokar hana zirga-zirga da aka sanya a birnin Dhaka. Shugabar an mata bore ne bayan wata doka da ta ƙirkiro wadda za ta ba da kasa 30 na ayyukan yi ga yan'uwa da kuma tsofaffin sojoji. Aƙalla mutane 300 ne suka rasa…
Read More
Ƴan sanda sun cafke telan da ke ɗinka tutar Rasha a Kano

Ƴan sanda sun cafke telan da ke ɗinka tutar Rasha a Kano

Ƴan sanda sun yi nasarar cafke wani tela mai suna Ahmed wanda ake tuhuma da ɗinka tutar ƙasar Rasha ya na rabawa mutane a yayin zanga-zanga. Kakakin rundunar ƴan sandan Olumuyiwa Adejobi ne ya sanar da hakan ta wani saƙon WhatsApp. Ya bayyana cewa an kama Ahmed ta tutar Rasha guda bakwai,wanda yake kira da cin amanar ƙasa da yi mata zagon ƙasa. Wannan na zuwa ne bayan jawabin da shugaban ƙasa yayi bai gamsar da mutane ba, sai a ka ga mutane sun fito su na ɗaga tutar ƙasar Rasha.
Read More
Ingancin man dizal ɗinmu daidai yake da na sauran duniya – Matatar Ɗangote

Ingancin man dizal ɗinmu daidai yake da na sauran duniya – Matatar Ɗangote

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Matatar Ɗangote ta sake tabbatar da cewa man dizal ɗin nata yana da inganci idan aka kwatanta da na ƙasashen waje da ake shigowa da shi, kuma ya cika ƙa'idojin ƙasa da ƙasa. Wannan dai na zuwa ne dangane da kalaman da babban jami’in hukumar kula da harkokin man fetur ta ƙasa, NMDPRA, Farouk Ahmed ya yi a baya-bayan nan, cewa ingancin man dizal ɗin ya yi ƙasa da wanda ake shigowa da su daga ƙasashen waje. An ruwaito matatar ta ce, babu ɗaya daga cikin man dizal da ake shigowa da shi Nijeriya da zai…
Read More
Rashin jituwa tsakanin Matatar Ɗangote da NMDPRA abin damuwa ne – Atiku

Rashin jituwa tsakanin Matatar Ɗangote da NMDPRA abin damuwa ne – Atiku

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar ya bayyana rashin jituwa tsakanin matatar mai ta Aliko Dangote da Hukumar Haƙowa da Sarrafa ɗanyen Mai ta Nijeriya (NMDPRA) a matsayin abin damuwa. A wani saƙon da ya wallafa a shafinsa na ɗ a ranar Talata, Atiku ya bayyana matatar Dangote a matsayin babbar hanyar zuba jari mai zaman kanta a ƙasar wanda ke da muhimmanci ga tattalin arzikin Njeriya. Atiku ya ce, kare manyan jari kamar matatar mai ta Aliko Dangote da ke Legas na da matuƙar muhimmanci wajen jawo hannun jarin ƙasashen waje zuwa cikin ƙasar, yana…
Read More
CBN ya sayar da Dala miliyan 148 ga ’yan canji masu lasisi

CBN ya sayar da Dala miliyan 148 ga ’yan canji masu lasisi

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Babban Bankin Nijeriya, wato CBN, ya ce ya sayar da jimillar dala miliyan 148 ga 'yan canji masu lasisi a kasuwar canjin kuɗaɗe ta Nijeriya (NFEM). A cewar Mrs Hakama Sidi-Ali, mukaddashin Darakta, Sashen Sadarwa na Kamfanin na Babban Bankin, an gudanar da hada-hadar ne a ranakun Litinin, 22 ga watan Yuli da Talata, 23 ga watan Yuli, 2024, tsakanin farashin canjin N1470.00/$1 zuwa N1510.00. /$1 don samar da ruwa ga kasuwar Fɗ Sidi-Ali ya kuma bayyana cewa, CBN ya sayar da Fɗ ga bankunan dillalai 29 masu izini a kan farashin canji tsakanin N1,470 zuwa…
Read More
Hukumar Kwastom ta dakatar da harajin shigo da kayan abinci

Hukumar Kwastom ta dakatar da harajin shigo da kayan abinci

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Hukumar Kwastam ta Nijeriya ta dakatar da haraji kan kayayyakin abinci da ake shigowa da su ƙasar. Hakan ya fito ne a wani faifan bidiyo da shugaban hukumar kwastam, Bashir Adewale Adeniyi ya wallafa a shafin X, inda ya ce an dakatar da shi ne domin bai wa 'yan Nijeriya damar samun wadataccen kayan abinci. Ya ƙara da cewa, hauhawar farashin kayayyaki a duniya yana shafar ƙasashe ciki har da Nijeriya, yana mai cewa hukumar ta himmatu wajen aiwatar da umarnin gwamnatin tarayya na dakatar da haraji kan muhimman kayayyaki.  “Hauhawar farashi a duniya yana shafar…
Read More
NACOTAN ta buƙaci a samar da masaƙu a Nijeriya

NACOTAN ta buƙaci a samar da masaƙu a Nijeriya

Daga MAHDI M. MUHAMMAD ƙungiyar Auduga ta Nijeriya (NACOTAN) ta yi kira da a kafa majalisar auduga, masaƙu da tufafi (CTG) domin daidaita al'amuran tattalin arziki a ƙasar. Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwar manema labarai da ƙungiyar ta fitar ranar Talata a Abuja bayan wani taron ƙara wa juna sani na kwana ɗaya da ya ƙunshi manyan masu ruwa da tsaki, inda aka tattauna kan manufofin CTG. Sanarwar ta fito ne ta hannun Shugaban NACOTAN, Hamma Kwajaffa, shugaban ƙungiyar masu masana’anta ta Nijeriya, Samuel Oloruntoba da babban sakataren ƙungiyar auduga. Sauran waɗanda suka rattaba hannun sun haɗa…
Read More
PAN ta nemi tallafin gwamnati don farfaɗo da kasuwancinta

PAN ta nemi tallafin gwamnati don farfaɗo da kasuwancinta

Daga MAHDI M. MUHAMMAD ƙungiyar Masu Kiwon Kaji ta Nijeriya (PAN), reshen Babban Birnin Tarayya, Abuja, ta buƙaci gwamnatin tarayya da hukumar Abuja da su taimaka wa mambobin da bala’i ya shafa domin farfaɗo da sana’o’insu. Pius Aminu, Shugaban PAN, reshen babban birnin tarayya, ya yi wannan roƙo a wata hira da Kamfanin Dillancin Labaran Nijeriya (NAN) a Abuja ranar Talata. Aminu ya ce, gyara masu kiwon kaji zai kare masana’antar daga durƙushewa. Idan za a iya tunawa, guguwar ruwan sama ya lalata wasu gidajen kiwon kaji a ƙananan hukumomin Kuje da Kwali a Abuja, a lokacin daminar bara. Shugaban…
Read More
Muna fuskantar ƙalubale a jagorancin kasuwar gwarin Illeoko a Legas – Mu’awuya Simoli

Muna fuskantar ƙalubale a jagorancin kasuwar gwarin Illeoko a Legas – Mu’awuya Simoli

Daga DAUDA USMAN a Legas  Wani babban mai faɗa a ji a kasuwar gwarin Illeoko ta Ƙaramar Hukumar Alimosho dake cikin birnin Ikko, Alhaji Mu'awuya Idris Simoli ya bayyana cewar shi da sauran shuwagabannin kasuwar ta gwarin Illeoko suna fuskantar manyan ƙalubale mai yawa a kasuwar da kewayenta gaba ɗaya. Alhaji Mu'awuya Idris Simoli ya furta hakan ne a Legas a lokacin da yake zantawa da jaridar Blueprint Manhaja dangane da al'amuran da suka shafi harkokin kasuwancin gwari a Legas baki ɗaya. Simoli ya ci gaba da labarta wa Jaridar Blueprint Manhaja cewar haƙiƙa tun daga wancan lokacin ya zuwa…
Read More