Kasuwanci

Gwamnati ta yi watsi da shirin karin kudin wutar lantarki

Gwamnati ta yi watsi da shirin karin kudin wutar lantarki

Daga BASHIR ISAH Gwamnatin Tarayya ta yi tsayin daka kan kin amicewa da karin farashin wutar lantarki kamar yadda kamfanin samar da lantarki na Nijeriya ya bukata. Ministan Makamashi, Adebayo Adelabu, shi ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Litinin. Ministan ya jaddada kudurin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu na tabbatar da wadatacciyar wutar lantarki a kasa. Adelabu ya kara da cewa, “Rashin damarmaki na ci gaba da zama babban kalubalen da fannin lantarki ke fuskanta. “Muna yin nazari kan tsarin aiwatar da jadawalin kuɗin fito tare da tabbatar da ci…
Read More
Kasafin 2024: Gwamna Lawal ya ware N1.3b don zamanatar da kafafen yaɗa labarai mallakar gwamnati

Kasafin 2024: Gwamna Lawal ya ware N1.3b don zamanatar da kafafen yaɗa labarai mallakar gwamnati

Daga BASHIR ISAH Gwamnatin Jihar Zamfara ta ware Naira biliyan 1.3 a kasafinta na 2024 don zamananta kafafen yada labarai mallakar jihar. Kwamishinan Yada Labarai da Raya Al'adu na Jihar, Mannir Haidara, shi ne ya bayyana haka ranar Litinin a Gusau, babban birnin jihar, jim kadan bayan gabatar da kasafin ma'aikatarsa ga Kwamitin Kudi na Majalisar Dokokin jihar. Kwamishinan ya jaddada cewa zamanantar da kafofin yada labarai mallakar jihar ya yi daidai da kudurin Gwamna Lawal na farfado da masana'antar yada labarai ta jihar. Ya kara da cewa, Kamar yadda aka sani, ma'aikatar ke da alhakin yada labarai a fadin…
Read More
Abubuwa 3 masu dakatar da nasarar mai sana’a – Likitan Sana’a

Abubuwa 3 masu dakatar da nasarar mai sana’a – Likitan Sana’a

Daga AMINA YUSUF ALI Ga wasu shawarwari da Badamasi Aliyu Abdullahi ya bayar ga masu sana'a don samun cigaba. Kamar yadda muka sani, kowacce cuta da maganinta. Don haka wasu abubuwa uku da Likitan sana'a ya rawaito cewa idan an guje su za a samu nasara a sana'ar da ake yi. Na farko, jiran tallafin gwamnati wanda ba ka san ranar zuwan sa ba: Masu sana'a da yawa suna tafka wannan kuskuren. Wasu kafin fara sana'arsu. Wasu bayan sun fara. Ga duk mai sana'a, babban strategy ɗin da za ka dauka da zai taimake ka shi ne, kar ka tsara…
Read More
Ya kamata gwamnatin tarayya ta haramta shigowa da tsofaffin motoci Nijeriya – (NADDC)

Ya kamata gwamnatin tarayya ta haramta shigowa da tsofaffin motoci Nijeriya – (NADDC)

Daga AMINA YUSUF ALI Hukumar tsarawa da kera motoci ta Nijeriya ta yi kira ga gwamnatin Tarayya a kan ta haramta shigo da tsofaffin motoci da aka yi amfani da su daga shekarar 2000 zuwa 2007 cikin Nijeriya. Jaridar Persecondnews ta rawaito cewa, bayanan da aka samu a binciken Hukumar kasuwancin Kasa da kasa a Amurka ta samar, ya bayyana cewa, bukatar ababen hawa/motoci a Nijeriya na kowacce shekara ta tasam ma guda 720,000 yayin da masana'antu na cikin gida suke iya samar da guda 14,000 kacal a kowacce shekara. Don haka ake shigo da ƙari wasu motocin don a…
Read More
Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa zai sanya baki don hana Shoprite barin Jihar Kano

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa zai sanya baki don hana Shoprite barin Jihar Kano

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Mataimakin shugaban majalisar dattawa, Sanata Barau I. Jibrin (Maliya), zai sanya baki don dakatar da yunkurin da katafaren shagon hada-hadar kasuwanci na Shoprite ya dauka na rufe reshensa daya tilo a jihar Kano. Katafaren kantin sayar da kayayyakin dake Ado Bayero Mall a Kano, a makon da ya gabata sun sanar da matakin ficewa daga cibiyar kasuwanci a watan Janairun da zai kama, inda suka bayyana cewa hakan ya biyo bayan yanayi na kalubalen tattalin arziki da ake fuskanta. An samu ra'ayoyi daban-daban dangane da matakin da Shoprite ta dauka wadda ke aiki a jihar…
Read More
CBN ya dakatar da cajin da bankuna kan yi wa kostomomi yayin ajiyar kuɗaɗe

CBN ya dakatar da cajin da bankuna kan yi wa kostomomi yayin ajiyar kuɗaɗe

Daga BASHIR ISAH Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya dakatar da harajin da akan karɓa yayin da kostomomi suka kai kuɗi mai yawa ajiya a banki. Hakan na ƙunshe ne cikin sanarwar da Muƙaddashin Daraktan Sanya Ido, Dr Adetona Adedeji, ya fitar a ranar Litinin. “Dukkanin bankunan da ke ƙarƙashin kulawar CBN su ci gaba da karɓar ajiyar kostomominsu ba tare da sun caje su komai ba," in ji CBN. Bankin ya kuma buƙaci bankuna da su bi wannan umarnin nasa sau da ƙafa. Sanarwar ta ce sabuwar dokar da aka samar a Disamban 2019, mai lamba FPR/DIR/GEN/CIR/07/042, ita ce ta…
Read More
Gwamnatin Tarayya ta ci burin ninninka kuɗin fetur zuwa Naira tiriliyan 7.69 a shekarar 2024

Gwamnatin Tarayya ta ci burin ninninka kuɗin fetur zuwa Naira tiriliyan 7.69 a shekarar 2024

Daga AMINA YUSUF ALI Gwamnatin Tarayya ta ci burin ninninka kuɗaɗen shiga da take samu ta hanyar man fetur har ninki uku wato zuwa Naira tiriliyan 7.69 a shekarar 2024 domin ta samu damar cikashe wani vangare na kasafin kuɗin ƙasa na shekarar 2024 wanda ya kai har kimanin Naira triliyan 27.5. A cewar wani lissafi da hasashe a game da gabatar da daftarin ƙudurin kasafin kuɗin ƙasar nan na 2024 wanda ministan kasafin kuɗi da tsare-tsaren tattalin arziki, Abubakar Atiku Bagudu ya gabatar, ya nuna cewa hasashen kuɗin shigar da za a samu a ɓangaren man fetur a 2024…
Read More
Rahoton bincike: Jihohi 10 da suka yi zarra wajen cin bashi a Nijeriya

Rahoton bincike: Jihohi 10 da suka yi zarra wajen cin bashi a Nijeriya

Daga AMINA YUSUF ALI A cikin shekarar bana ta 2023 Nijeriya ta fuskanci ƙalubale da dama da yake da alaƙa da tattalin arzikin ƙasar. Wannan dalili ya sa wasu jihohi da dama a Nijeriya suka dulmiya tsundum a cikin tarkon bashi. Jaridar Ingilishi ta The Spectacles ta yi bincike da nazari a kan wasu jihohi guda 10 da suka fi kowaɗanne ciyo bashi a Nijeriya. Legasa (Naira triliyan 1.97) Ta farko a cikin jerin ita ce jihar Legas wacce take a Kudancin Nijeriya. Jihar Legas ta jagoranci wannan jeri ne na jihohi masu kan bashi ne saboda bashin da ta…
Read More
Kashi 70 na ma’aikatan kamfanin Mamuda ‘yan Kano ne – Gaddafi

Kashi 70 na ma’aikatan kamfanin Mamuda ‘yan Kano ne – Gaddafi

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano Gaddafi Isyaku Hassan, jami'in cinikayya na kamfanin Mamuda, ya ce suna bada gudunmuwa ga mata domin ƙara musu ƙwarin gwiwa wajen sana'ar dogaro da kai, tarbiyya a zamantakewarsu na rayuwar aure a tarukansu daban-daban. Ya bayyana hakan ne ga manema labarai a wani taro da wasu mata suka gudanar da kamfanin ya bajekolin kayyakinsa da makarantu don qara musu ƙwarin gwiwa. Jami'in ya ce irin gudummuwar da suke bayarwa bai tsaya ga cigaban mata kaɗai ba har da ɓangaren ilimi har sai da ma'aikatar ilimi ta jihar Kano ta karramasu bisa irin jajircewa da  taimako…
Read More
Idan ka na sana’a ba ka da wannan tunani, kai da cigaba sai a mafarki – Likitan sana’a

Idan ka na sana’a ba ka da wannan tunani, kai da cigaba sai a mafarki – Likitan sana’a

Daga AMINA YUSUF ALI Malam Badamasi Aliyu Abdullahi masani ne a kan dabarun tafiyar da sana'a da tattalin arziki. Ga wasu shawarwari da ya bayar a kan sana'a kamar haka: Son koyo  da neman ilimi. Masu sana'a da ke da aƙida ta son cigaba suna son koyo ko sanin wani sabon abu da ya danganci harkar sana'arsu. Sun yarda cewa duniya kullum cigaba ake samu kuma cigaba a harkokin kasuwanci yana da kyakkyawar alaƙa da neman ilimi sana'a, fahimtar tattalin arziƙi, fahimtar ƙudurorin gwamnati, koyon amfani da sabbin dabaru, sabbin kayan aiki da sauransu.  2. Kallon ƙalubale a matsayin taki.…
Read More