27
Jul
Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Ƙasashe 58 daga cikin 164 mambobin Ƙungiyar Cinikayya ta Duniya (WTO) sun nuna goyon bayansu ga buƙatar neman shugabar ƙungiyar Ngozi Okonjo-Iweala ta yi tazarce wa'adi na biyu. Ƙasashen sun bayyana goyon bayansu ne ga Okonjo-Iweala a babban taron ƙungiyar da aka gudanar ranar Litinin, kamar yadda WTO ta wallafa a shafinta na intanet. "Ƙungiyar Afirka da ake kira Africa Group ne ta gabatar da buƙatar cewa shugabar a shirye take ta yi wa'adi na biyu, kuma ta gabatar da buƙatar cewa a fara bin matakai na sake zaɓar ta ba tare da ɓata…
