Kasuwanci

Ƙasashen duniya 58 na son Ngozi Okonjo-Iweala ta yi tazarce a WTO

Ƙasashen duniya 58 na son Ngozi Okonjo-Iweala ta yi tazarce a WTO

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Ƙasashe 58 daga cikin 164 mambobin Ƙungiyar Cinikayya ta Duniya (WTO) sun nuna goyon bayansu ga buƙatar neman shugabar ƙungiyar Ngozi Okonjo-Iweala ta yi tazarce wa'adi na biyu. Ƙasashen sun bayyana goyon bayansu ne ga Okonjo-Iweala a babban taron ƙungiyar da aka gudanar ranar Litinin, kamar yadda WTO ta wallafa a shafinta na intanet. "Ƙungiyar Afirka da ake kira Africa Group ne ta gabatar da buƙatar cewa shugabar a shirye take ta yi wa'adi na biyu, kuma ta gabatar da buƙatar cewa a fara bin matakai na sake zaɓar ta ba tare da ɓata…
Read More
Matatar man Ɗangote za ta riƙa sayo ɗanyen mai daga Libya da Angola

Matatar man Ɗangote za ta riƙa sayo ɗanyen mai daga Libya da Angola

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Matatar mai ta Ɗangote da ke jihar Legas a Nijeriya ta fara tattaunawa da ƙasar Libya domin sayen ɗanyen man fetur da za ta dinga tacewa na ganga 650,000 a kullum. Kamfanin labarai na Reuters ya kuma ruwaito cewa matatar, wadda attajiri mafi arziki a Afirka ya mallaka Aliko Ɗangote, tana yunƙurin sayo ɗanyen man daga ƙasar Angola. Matakin na zuwa ne yayin da Ɗangote ke yunƙurin kauce wa ƙarancin man da yake fuskanta duk da ɗimbin arzikin man da Nijeriya ke da shi, inda a gefe guda kuma hukumar kula da harkokin man…
Read More
Abubuwan da suke nuna ka samu sana’a mai kyau – Likitan Sana’a

Abubuwan da suke nuna ka samu sana’a mai kyau – Likitan Sana’a

Daga AMINA YUSUF ALI A tattaunawarmu da Badamasi Aliyu Abdullahi wanda aka fi sani da likitan sana'a, wanda ƙwararre ne a kan sanin madafa da mafita a game da sana'o'i da dabarun bunƙasa tattalin arziki. Ya bayyana mana wasu hanyoyi da mai sana'a zai gane cewa sana'ar da yake ciki ko aikin da yake yi sana'a ce ko aiki ne mai kyau da ya dace da shi. A tattaunawar ga wasu dalilai da ya kawo. Idan kana shauƙin ta. Son sana'arka shi ne tubalin gina ta da yin haƙuri da juriya da kasuwanci ke buƙata. Idan ba soyayyar abinda ka…
Read More
Gwamnatin Kaduna za ta tallafi manoman citta a jihar

Gwamnatin Kaduna za ta tallafi manoman citta a jihar

Daga AMINA YUSUF ALI Rahotanni sun bayyana cewa, Gwamnatin Kaduna tare da hukamar gwamnatin Tarayya za su tallafa wa manoman citta da suka tafka hasara a kakar bara Gwamnatin Kaduna tare da hukamar gwamnatin Tarayya za su tallafa wa manoman citta da suka tafka hasara a kakar baraBiyo bayan ibtila’in da ya afka wa manoman Citta da ya yi sanadiyyar tafka gagarumar asara a kakar noman bara da wasu manoman suka rasa ilahirin amfanin gonarsu, jin ƙai da tallafi na tafe cikin gaggawa daga mahukunta daga Kaduna da gwamnatin Tarayya. Asusun tallafa wa manoma na gwamnatin tarayya NADF da hukumar…
Read More
Ana sa ran ƙasashen Mali, Burkina Faso da Nijar za su janye ficewa daga ECOWAS – Ndume

Ana sa ran ƙasashen Mali, Burkina Faso da Nijar za su janye ficewa daga ECOWAS – Ndume

Daga AMINA YUSUF ALI Rahotanni dai sun bayyana cewa, ƙasashen Mali, Burkina Faso da Nijar na shirin janye matakinsu na ficewa daga ƙungiyar Ecowas mai raya tattalin arzikin qƙasashen Afirka ta Yamma. Sanata Ali Ndume - wanda ɗan majalisar ƙungiyar Ecowas ɗin ne ya bayyana haka yayin zantawa da manema labarai a Kano, a yayin da majalisar ƙungiyar ke ci gaba da gudanar da taronta a jihar. Dan majalisar ya ce an cimma duk wani abu da ake buƙata domin maido da ƙasashen cikin ƙungiyar ta Ecowas. "An riga an warware saɓanin da ya kai ga ɗaukar matakin fita daga…
Read More
Mafi ƙarancin albashi: NLC ta ƙara matsa lamba a kan gwamnatin Tarayya

Mafi ƙarancin albashi: NLC ta ƙara matsa lamba a kan gwamnatin Tarayya

Daga AMINA YUSUF ALI Ƙungiyoyin 'yan ƙwadago ta NLC da TUC sun nemi gwamnatin Bola Ahmad Tinubu da ta biya Naira 497,000 maimakon Naira 615,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi. A taqaice dai ma wato sun sassauta abin da suke buƙata gwamnati ta biya a matsayin mafi ƙarancin albashi a ƙasar zuwa naira 497,000. A baya dai ƙungiyoyin ƙwadagon sun ce dage a kan Naira 615,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi da suke son gwamnatin ƙasar ta amince da shi. Yayin cigaba da tattaunawar a ranar Talatar da ta gabata, ƙungiyoyin sun kuma yi watsi da sabon ƙudirin da gwamnati…
Read More
Gwamnati ta dakatar da jirgin Air Nigeria har sai baba-ta-gani

Gwamnati ta dakatar da jirgin Air Nigeria har sai baba-ta-gani

Gwamnatin Tarayya ta ba da sanarwar cewa, ta dakatar da aikin kamfanin jirgin saman Nijeriya, wato Air Nigeria. Sanarwar wadda aka fitar a ranar Litinin ta ce, dakatarwar ta har baba-ta-gani ce. Ministan Sufurin Jirgin Sama, Festus Keyamo, shi ne ya bayyana haka yayin da yake ba da bayani kan ayyukan ma'aikatarsa a matsayin ɓangare na cika Shuga Bola Tinubu shekara guda a ofis. Da yake ƙarin haske kan dalilin dakatarwar, Keyamo ya ce, jirgin da aka nuna cewa ta Nijeriya ne ba gaskiya, rufa-rufa ce kawai aka yi wa lyan ƙasa a wancan lokaci.
Read More
Tinubu ya bai wa fasinjoji alakoron wata biyu a sabon jirgin ƙasan Abuja

Tinubu ya bai wa fasinjoji alakoron wata biyu a sabon jirgin ƙasan Abuja

Daga WAKILINMU A yayin da aka kammala shirye-shiryen buɗe tashar sabon jirgin ƙasan Abuja a ranar 29 ga watan Mayu, Ministan babban birnin, Nyesom Wike, ya shaida wa manema labarai cewa tuni Shugaba Tinubu ya buƙaci da a ɗebi fasinjoji kyauta na tsayin wata biyu a jirgin ba tare da an karɓi ko sisinsu ba. Hakan na zuwa ne a yayin da Gwamnatin Tarayya ta ce ta sami ragin Dala Milyan 53 a aikin wanda a ka kammala shi a kan kuɗi Dala milyan 75 maimakon Dala milyan 128 da gwamnatin baya ta ce za a yi aikin. Ministan ya…
Read More
Ƙwarewa a sana’a ita ce gaba da samun digiri – Dogondaji

Ƙwarewa a sana’a ita ce gaba da samun digiri – Dogondaji

Daga AMINA YUSUF ALI A yayin da kafafen yaɗa labarai suke ci gaba da tafka muhawara game da fififkon ilimin digiri a kan sana'a, mun samu zantawa da Malam Yahya Dogondaji wanda matashi ne wanda ya yi wa 'yanuwansa matasa zarra wajen yaƙi da talauci, ta hanyar yi wa kansa fafutuka da kuma horas da matasa masu dama a ƙarƙashin sana'ar sa ta gyaran waya da kuma samar da guraben ayyuka ga matasa da dama. Hakazalika, ya kasance mai tallafa wa marasa galihu ta gidauniyarsa. Wakiliyar MANHAJA BLUEPRINT, Amina Yusuf Ali ta samu tattaunawa da Malam Yahya Dogon daji, kuma…
Read More