Kasuwanci

NARTO suna ƙoƙarin wajen wayar da kan direbobi – Muhammad Inuwa

NARTO suna ƙoƙarin wajen wayar da kan direbobi – Muhammad Inuwa

Daga MUHAMMADU MUJITTABA a Kano Alhaji Muhammad Inuwa Sakataren Ƙungiyar Masu Motocin Sufuri na Ƙasa, rashen Jihar Kano ya bayyana cewa, ƙungiyar su ta NARTO na taka muhimmiyar rawa wajen ganin ma'aikatan su sun bi duk kanin ƙa'idojin tuqi da kuma kula da lafiyar ababan hawan su a koda yaushe domin ganin an rage munanan haɗurran da akan samu akan hanyoyinmu na Nijiriya musamman a watanni huɗu ƙarshen kowacce Shekara. Kamar dai yadda sakataren ƙungiyar NARTO na Kano ya bayyana a lokacin taron wata ƙungiya mai suna MAMA da ta shirya don wayar da kan masu tuƙa ababan hawa da…
Read More
Sai an tallafa wa ƙananan masana’antu idan ana son karya farashin shinkafar gida – Ambasada Ali

Sai an tallafa wa ƙananan masana’antu idan ana son karya farashin shinkafar gida – Ambasada Ali

Daga MUHAMMADU MUJITTABA a Kano Ambasada Alhaji Ali Idris Mai Unguwa Kura, Shugaban Ƙungiyar Masu Sarrafa Shinkafa, Sayarwa da Noma ta na Ƙaramar Hukumar Kura, kuma Shugaban Ƙungiyar Masu Ƙananan Masana'antu da Matsakaita na Sarrafa Shinkafa na Ƙasa, reshan Jihar Kano, ya bayyana cewa ƙorafi da koke-koke da ake yi na tsadar shinkafa, wannan ya samo asali ne daga ƙarancin masu sarafa ta. Alhaji Ali ya ƙara da cewa, "idan har ana son noma shinkafa ya bunƙasa cikin tsafta, ya kuma wadata, da babu tsakuwa ko ƙuƙus, a cikin ta cikin farashi mai sauƙi da rahusa, sai an tallafawa ƙanana…
Read More
Tinubu ya nemi Jamus ta saka hannun jari a fannin makamashi da layin dogo

Tinubu ya nemi Jamus ta saka hannun jari a fannin makamashi da layin dogo

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaba Bola Tinubu ya yi kira ga ƙasar Jamus da ta saka hannun jari a fannonin tattalin arzikin Nijeriya masu muhimmanci kamar wutar lantarki da sufurin jiragen ƙasa. Wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ƙasar Ajuri Ngelale, ya fitar, ta ce Mista Tinubu ya yi wannan kiran ne a wani taro da shugaban gwamnatin Jamus Olaf Scholz, a taron G20 Compact with Africa Economic Conference, ranar Litinin a Berlin. Shugaban ya ce ana buƙatar zuba jarin Jamus a cikin muhimman masana'antu masu samar da ci gaba a fannin makamashi, sufuri, da samar…
Read More
Google ya bayar da gargaɗin mako uku ga masu amfani da Gmail

Google ya bayar da gargaɗin mako uku ga masu amfani da Gmail

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Kwanan nan Google ya ba da gargaɗi na makonni uku ga masu asusun Gmail, wanda ke nuna alamar share miliyoyin asusun a wata mai zuwa a matsayin wani ɓangare na sabunta dandamali. Wannan yunƙurin zai shafi duk asusun Google waɗanda ba a yi amfani da su ba aƙalla shekaru biyu, wanda ya haifar da cire imel na dindindin, takardu, maƙunsar bayanai, alƙawuran kalanda, hotuna, da bidiyoyi. Sabuwar manufar, wacce aka gabatar a farkon wannan shekarar, an tsara ta fara aiki a watan Disamba na 2023. Babban maƙasudin da ke bayan wannan yunqurin shi ne don haɓaka…
Read More
An buƙaci Gwamnatin Tarayya ta yi amfani da kuɗaɗen Abacha wajen cigaban matasa

An buƙaci Gwamnatin Tarayya ta yi amfani da kuɗaɗen Abacha wajen cigaban matasa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Joseph Effiong, Shugaban Yaxa Labarai na UpdateAfrika Communications ya buƙaci Gwamnatin Tarayya da ta yi amfani da dala miliyan 150 da tsohon shugaban mulkin sojan Nijeriya Sani Abacha ya wawashe inda wajen cigaban matasan Nijeriya, da zarar Faransa ta sake kuɗaɗen. Effiong ya ce, kamata ya yi gwamnati ta mutunta shawarar da Faransa ta bayar na tura kuɗaɗen zuwa ayyukan raya ƙasa, kuma kada ta bari ya tafi yadda ya tafi a baya. Da ta ke magana game da kuɗaɗen Abacha, Catherine Colonna, ministar Turai da harkokin wajen Faransa, ta ce mayar da kuɗaɗen zai biyo…
Read More
Za mu haɗa kai da sarakunan gargajiya domin daƙile matsalar tsaro – Tinubu

Za mu haɗa kai da sarakunan gargajiya domin daƙile matsalar tsaro – Tinubu

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaban Ƙasa Bola Tinubu, a ƙarshen mako ya ce gwamnatinsa za ta haɗa kai da sarakunan ƙasar nan domin tabbatar da ci gaba da kawo ƙarshen rashin tsaro. Tinubu ya bayyana haka ne a yayin bikin cika shekaru 70 da haihuwar Osemawe na masarautar Ondo, Oba Victor Kiladejo, wanda aka gudanar a Cocin Diocese of Ondo (Anglican Communion) Cathedral Church na St. Stephen a cikin birnin Ondo. Shugaban wanda ya samu wakilcin Ministan Harkokin Cikin Gida, Mista Olubunmi Tunji-Ojo, ya ce haɗin gwiwar ya zama wajibi domin zaman lafiya da kwanciyar hankali su karaɗe…
Read More
Yadda za mu inganta sana’armu don yaƙi da talauci

Yadda za mu inganta sana’armu don yaƙi da talauci

Tare da ABBA ABUBAKAR YAKUBU Kamar da wasa aka fara sanya hotunan kayan sayarwa da sana'o'i a zaurukan sada zumunta, ana aikawa da wanda aka saya, bayan an biya kuɗin ta banki, a motocin haya ko ta hannun wasu amintattu, yanzu wannan hanyar tallata kasuwanci ta zama babbar harka da miliyoyin ’yan kasuwa maza da mata ke samun kuɗaɗe masu yawa da abin rufin asiri. Da dama daga cikin waɗanda suke wannan kasuwanci ko dillanci, basu da rumfa ko shago, a gida suke ajiye kayansu, sai an saya sannan su fitar da shi zuwa tasha. Wasu kuwa ma ba su…
Read More
CBN ya shure wa’adin daina amfani da tsoffin takardun Naira

CBN ya shure wa’adin daina amfani da tsoffin takardun Naira

Daga BASHIR ISAH Babban Bankin Nijeriya (CBN), ya tsawaita wa'adin amfani da tsaffin takardun Naira, N200, N500 da kuma N1,000 har illa ma sha'a. Daraktan sashen sadarwar bankin, Isa AbdulMumin, shi ne ya bayyana haka cikin sanarwar da ya fitar ranar Talata mai taken, “CBN zai bada damar ci gaba da amfanin da tsaffin takardun Naira a dokance." Sanarwar ta ce an ɗauki wannan mataki ne daidai da yadda hada-hadar kuɗaɗe ke gudana a ƙasashen duniya. Idan za a iya tunawa, a Oktoban 2022 ne CBN ya ƙaddamar da sabbin takardun kuɗi na N200, N500 da N1000, sannan ya yanka…
Read More
Bankin Musulunci zai kashe wa Nijeriya biliyoyin Dala

Bankin Musulunci zai kashe wa Nijeriya biliyoyin Dala

Daga BASHIR ISAH Bankin Bunƙasa Musulunci (UDB) ya shirya zai kashe wa Nijeriya biliyoyin Dalar Amurka domin aiwatar da ayyukan cigaban ƙasa. Mai magana da yawun Shugaban Ƙasa, Ajuri Ngelale ne ya bayyana haka ranar Talata. Ya ce tallafin ɓangare ne na ribar tattaunawar zuba jari da Shugaba Tinubu ya yi da Mataimakin IDB, Dr. Mansur Muhtar, yayin da suka haɗu a Makka, Saudiyya. A cewar Ajuri, yayin tattaunawar tasu, Tinubu ya ce, "Nijeriya fitila ce da za ta haskaka wa sauran ƙasashen Afirka hanya, kuma da zarar Afirka ta ɗau haske, duniya za ta yi wa al'umma daɗin zama."…
Read More
Ba mu bayar da umarnin janye tsofaffin takardun kuɗin Naira ba – CBN

Ba mu bayar da umarnin janye tsofaffin takardun kuɗin Naira ba – CBN

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Babban Bankin Nijeriya (CBN), ya ce duk takardun kuɗi (tsofaffi da sababbi) suna nan a kan doka. Wannan na zuwa ne sakamakon fargabar da ake ciki cewa tsofaffin takardun kuɗi za su daina aiki nan da watan Disamba 2023. Wata sanarwar da mai magana da yawun bankin CBN, Isah Abdulmunin ya fitar a ranar Laraba, ta ce bankin bai bayar da umarnin janye tsofaffin takardun kuɗi ba daga wajen al'umma. Bankin ya ce, “An kuma samu rahotannin damuwa da wasu jama’a ke nunawa kan halacci ko rashinsa na tsoffin takardun kuɗin Naira. “Don kauce wa shakku,…
Read More