28
Apr
Daga MAHDI M. MUHAMMAD Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta ce, za ta duba batun ƙarin farashin da kamfanin MultiChoice, mamallakin tashoshin tauraron ɗan adam na DSTv da GOTv, ya yi kwanan nan ta hanyar masu ruwa da tsaki don tabbatar da walwawar Nijeriya da kuma ganin cewa sun more kuɗin su. Muƙaddashin Shugaban Hukumar Kula da Masu Sayayya ta Tarayya (FCCPC), Adamu Abdullahi, ya bayyana haka a gidan Talabijin na Channels a Abuja ranar Alhamis. A yayin tattaunawar, ya bayar da cikakken bayani kan sammacin da aka yi wa wani kantin sayar da kayayyaki na ƙasar Sin da ke Abuja da…
