Kasuwanci

An horar da ƙananan ‘yan kasuwa 102 dabarun inganta sana’o’i na zamani

An horar da ƙananan ‘yan kasuwa 102 dabarun inganta sana’o’i na zamani

Daga MUHAMMADU MUJJITABA a Kano Ƙwararru kan harkokin kasuwancin da suka fito daga ɓangarori daban-daban sun shawarci ƴan kasuwa da masu ƙananan masana'antu su rungumi sabbin hanyoyin kasuwanci da fasahar sadarwa ta zamani, domin bunƙasa sana'o'insu. An yi wannan kiran ne a wajen taron da Dandalin Horarwa Kan Dabarun Sana'o'in Zamani na Mu Inganta Sana'armu wanda ya gudana a birnin Kano, da nufin wayar da kan ƙananan ƴan kasuwa, da samar da muhallin da za su baje-kolin sana'o'insu, don sabbin abokan hulɗa da ƙulla ƙawance tsakanin ƴan kasuwa da masu masana'antu. Taron Mu Inganta Sana'armu wanda shi ne irinsa na…
Read More
Gidauniyar Isah Wali ta jagoranci ƙungiyoyi wajen koya wa masu tallace-tallace sana’o’i

Gidauniyar Isah Wali ta jagoranci ƙungiyoyi wajen koya wa masu tallace-tallace sana’o’i

Daga MUHAMMADU MUJJITABA a Kano Gidauniyar Isah Wali Empowerment Initiative IWEI ta gajoranci gamayyar ƙungiyoyi bakwai na tallafa wa al'umma musamam matasa mata da maza koyawa 'yan talla 50 a bakin titi mata da maza, sana'oi'n dogaro da kai domin rabasu da talla da barace-barace akan titi kamar dai yadda jami'ar ayyuka na musamman a gidauniyar IWEI Madam Bridget Idoko ta bayana a lokacin horas da 'yan talla 50 sana'o'in dogaro da kai da aka gabatar a makon da ya gabata a ɗakin karatu na Murtala Muhammad dake Kano. Daga cikin gamayyar qungiyoyin da suka horas da waɗannan matasa akwai…
Read More
Ƙarancin kuɗi: Ƙarin albashin ma’aikatan Gwamnatin Tarayya ya haɗu da tsaiko

Ƙarancin kuɗi: Ƙarin albashin ma’aikatan Gwamnatin Tarayya ya haɗu da tsaiko

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ana ƙara nuna damuwa kan yadda batun alƙawarin Gwamnatin Tarayya na ƙara wa ma’aikatanta albashin Naira 35,000 na tsawon watanni shida ke fuskantar ƙalubalen kuɗi. Bincike ya nuna cewa, Gwamnatin Tarayya ba ta da isassun kuɗaɗe da za ta cika alƙawarin da ta ɗauka na ƙara wa dukkan ma’aikatan tarayya albashi, alƙawarin da ta ɗauka a lokacin da aka cire tallafin man fetur a watan Mayun 2023. A lokacin da shugaban ƙasa Bola Tinubu ya rattaba hannu kan wata yarjejeniyar fahimtar juna da Ƙungiyoyin Kwadago ta Nijeriya NLC da TUC a ranar 2 ga watan Oktoba…
Read More
Bikin Magaji bai hana na Magajiya: Matsin tattalin arzikin Nijeriya bai hana Tinubu canza wa matarsa motoci ba 

Bikin Magaji bai hana na Magajiya: Matsin tattalin arzikin Nijeriya bai hana Tinubu canza wa matarsa motoci ba 

Daga AMINA YUSUF ALI  Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya bayyana, zai saya wa matarsa Remi motocin Naira biliyan 1.5, kuma shi ma zai sauya motocin ofishinsa da Naira biliyan 2.9. Duk da matsalar rashin kuɗdi da tsadar rayuwar da ake ta kuka, wadda gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ya jefa ‘yan Nijeriya bayan cire tallafin fetur, Tinubu zai sai wa Remi matarsa  motocin Naira biliyan 1.5, shi ma zai sauya motocin ofishinsa da Naira biliyan 2.9. Waɗannan Naira biliyan 2.9 kuwa, Gwamnatin Tinubu za ta kashe su ne wajen maye danƙara-danƙaran motocin Ofishin Shugaban ƙasa, waɗanda aka ci zamanin mulkin…
Read More
Fidelity Bank ya maido da zarafin tura kuɗi zuwa bankunan OPay, Kuda, Moniepoint da Palmpay

Fidelity Bank ya maido da zarafin tura kuɗi zuwa bankunan OPay, Kuda, Moniepoint da Palmpay

Daga BASHIR ISAH Bankin Fidelity ya maido da zarafin yin tiransifa ta yadda a yanzu kostomominsa za su iya ci caba da tura kuɗi zuwa bankuna irin su OPay da Moniepoint da Palmpay da kuma Kuda. Wannan na zuwa bayan da a 'yan makonnin da suka gabata Bankin Fidelity ya daƙile damar yin tiransifa zuwa wasu bankuna saboda yawaitar harkokin 'yan damfara da kuma tantance kostomominsa. Majiya daga bankin ta ce yanzu bankin ya buɗe hanyar ci gaba da tiransifa ta yadda a abokan mu'amalarsa za su ci gaba da tura kuɗi zuwa bankunan da a baya ya katse zarafin…
Read More
Kamfanin NNPCL ya gargaɗi masu ɓoye man fetur

Kamfanin NNPCL ya gargaɗi masu ɓoye man fetur

Daga AMINA YUSUF ALI Kamfanin man fetur na Najeriya, NNPCL, ya gargaɗi jama'ar ƙasar Nijeriya da su kiyayi sayen mai suna adanawa, don tsoron fuskantar ƙaranci da ƙarin farashin man. Wannan gargaɗi ya biyo bayan ƙaruwar jerin motoci ne a gidajen mai a sassan ƙasar a 'yan kwanakin nan. NNPC, ya ce yin gargaɗin ya zama wajibi, bisa la'akari da yadda aka fara ganin layukan ababen hawa a gidajen mai a birnin Ikko, cibiyar kasuwancin ƙasar, da birnin tarayya Abuja da dai sauran wasu garuruwa na Nijeriyar. Wata sanarwa da kamfanin man ya fitar, ta ba wa 'yan Najeriya tabbaci,…
Read More
Bankin Fidelity ya dakatar da tura kuɗi ta Opay da sauransu

Bankin Fidelity ya dakatar da tura kuɗi ta Opay da sauransu

Daga AMINA YUSUF ALI Bankin kasuwanci na Nijeriya, Bankin Fidelity ya toshe ƙananan bankuna kamar OPay, Palmpay, Kuda, da Moniepoint saboda rashin tantance masu ajiyarsu. Rashin sanin masu ajiya KYC na waɗancan ƙananan bankuna ya fiye sako-sako abinda yake jawo matsalar zamba a bankuna.  Wannan dalili ne ya sa banki na Fidelity ya toshe tiransifar kuɗi zuwa bankunan Moniepoint, Kuda, OPay, da PalmPay, a cewar wasu da suke da masaniya mai ƙarfi a kan lamarin.  A satin da ya gabata ne dai wasu masu ajiya da bankin Fidelity suka lura da cewa, an cire sunayen waɗancan ƙananan bankuna daga cikin…
Read More
Mahimmancin rubuta bayanan kasuwanci

Mahimmancin rubuta bayanan kasuwanci

Daga ZAUREN TASKAR NASABA Bayanan Kasuwanci (Record keeping) 'yan kasuwa masu yawa suna buƙatar ƙara sanin taskacewa ko rubuta bayanan kasuwanci abu ne mai matuƙar mahimmanci da kawo cigaban kasuwancin. Sai dai wasu cikin 'yan kasuwa basu ɗauki rubutun bayanan kasuwanci a matsayin abu mai amfani ba, don haka ba ruwansu da shi. Misali za ka samu ɗan kasuwa ya sayo atamfa a Kano a kan kuɗi N 9,000 ya ɗauke ta zuwa Adamawa ya sayar a kan Naira 9,500 yana tunanin ya ci ribar N500 wanda a zahiri haka ne, ya samu ribar N500. Amma ɗan kasuwa wanda yake…
Read More
Gwamnatin Tarayya ta ba da wa’adin shekaru biyar ga shigo da alkama Nijeriya

Gwamnatin Tarayya ta ba da wa’adin shekaru biyar ga shigo da alkama Nijeriya

Daga AMINA YUSUF ALI Ministan harkar noma da kiwo na Nijeriya, Abubakar Kyari, ya ba da wa'adin shekaru biyar ga Nijeriya ta daina shigo da alkama daga ƙasar waje. A cewarsa, hakan yana lamushe tanadin kuɗin wajen da Nijeriya ta yi. Kyari ya yi wannan bayani ne ga 'yan jaridu jim kaɗan bayan ya duba ingancin irin shukar alkama a Kano ranar Juma'ar da ta gabata. A cewar sa, ya gamsu da cewa, samar da abu a cikin ƙasa shi ne ƙashin bayan noma. Kuma a cewar sa, gwamnati tana ta ƙoƙari wajen ganin an daina shigo da tsabar alkama…
Read More
Nijeriya ta zama ƙasa ta 4 a jerin ƙasashe 10 mafiya amsar bashi a Bankin Duniya

Nijeriya ta zama ƙasa ta 4 a jerin ƙasashe 10 mafiya amsar bashi a Bankin Duniya

Daga AMINA YUSUF ALI A yanzu haka dai ƙasar Nijeriya ta taka matsayi na 4 na ƙasashen da suka fi kowa cin bashi a jerin sunayen ƙasashe na IDA na Bankin Duniya (ƙasashe masu yin rance a bankin). A yanzu haka ana bin ƙasar bashin Dalar Amurka biliyan 14.3. Nijeriya ta daɗe a wannan matsayi nata na huɗu a jerin ƙasashe da ke ƙungiyar (IDA) masu rancen. Tun bayan da ta baro matsayi na 5 a Yunin shekarar 2022. Duk da Nijeriya ta kasance mai matsayi na 4, ta tara wa kanta bashin Dalar Amurka biliyan 1.3 a cikin shekara…
Read More