Kasuwanci

Ramadan: ‘Ku sassauta farashin kayan abinci’ — kiran Sarkin Kano, Ado-Bayero ga ‘yan kasuwa

Ramadan: ‘Ku sassauta farashin kayan abinci’ — kiran Sarkin Kano, Ado-Bayero ga ‘yan kasuwa

Daga BASHIR ISAH Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado-Bayero, ya yi kira ga 'yan kasuwa da su sauke farashin kayan abinci da sauransu domin bai wa al'umma damar yin azumin Ramadan cikin walwala. Basaraken ya yi wannan kira ne a wajen taron ƙaddamar da littafi mai taken: “Dauloli a Ƙasar Hausa” wallafar Farfesa Sa’idu-Mohammed Gusau wanda ya gudana ranar Lahadi a Zaria. Kazalika, ya yi kira ga masu hannu da shuni da su dubi Allah su taimaka wa mabuƙata yayin watan na Ramadan. Ado Bayero ya yaba wa marubucin littafin bisa ƙoƙarin da ya yi wajen bayyana Masarautun Hausa da ke…
Read More
Uwargidan gwamnan Kebbi ta tallafa wa mata da Naira miliyan 10

Uwargidan gwamnan Kebbi ta tallafa wa mata da Naira miliyan 10

Daga JAMIL GULMA a Birnin Kebbi Uwargidan gwamnan Kebbi Hajiya Zainab Nasir ta tallafawa mata masu ƙananan sana'o'i da Naira milliyan goma a ƙarƙashin hukumar SMEDAN. Uwargidan Gwamnan ta bayar da wannan tallafin ne a lokacin da take halartar taron Ramadan Funfair da ya gudana ranar Lahadi a babban ɗakin taro dake Shugaban Ƙasa wato Presidential Lodge dake cikin garin Birnin Kebbi. Da take jawabi a wurin taron, uwargidan Gwamnan ta bayar da umarnin cewar dukkanin matan da suka halarci taron da sana'o'insu da a tabbatar sun samu wani kaso a cikin gudunmawar kuɗin da ta bayar. Haka kuma ta…
Read More
Maɗaba’ar Kano ta samu kayan aiki da za ta zama ta ɗaya a Arewa – DMD Adamu

Maɗaba’ar Kano ta samu kayan aiki da za ta zama ta ɗaya a Arewa – DMD Adamu

Daga MUHAMMADU MUJITABA a Kano Maɗaba'ar Gwamnatin Kano KPPC mai buga muhimman takardun sirrin gwanati da sauran takardun amfanin al'umma da wallafe-wallafe na gwamnati da na kamfanoni da sauran al'umma yanzu haka ta farfaɗo da ga dogon suman da ta yi na rashin aikin yi da rashin kayan aiki wanda yanzu ta samu kayan aikin da za ta iya zama ta ɗaya Arewacin Nijeriya kamar yadda Gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf yake son ganinta, wanda hakan ce tasa daga zuwansa ya ba su  dama da busa mata rai ta farfaɗo ta hanyar bada damar a cewa dukka abinda muke…
Read More
Akwai kyakkyawar alaƙa tsakanin NARTO da NURTW a Nasarawa – Muhammadu Maikwarya

Akwai kyakkyawar alaƙa tsakanin NARTO da NURTW a Nasarawa – Muhammadu Maikwarya

Daga JOHN D. WADA a Lafiya Sabon Shugaban Ƙungiyar Masu Motocin Sufuri, NURTW, na ƙasa reshen Jihar Nasarawa, Alhaji Muhammadu Maikwarya ya bayyana cewa, ba shakka kawo yanzu da ya kama aikinsa a matsayin sabon shugaban ƙungiyar ta Nasarawa ana cigaba da samun kyakkyawar dangantaka tsakanin ƙungiyar tasa da takwararta ta NARTO. Alhaji Muhammadu Maikwarya ya bayyana haka ne a lokacin da yake tattaunawa da wakilinmu a ofishinsa da ke hedikwatar NURTW a birnin Lafiya, fadar gwamnatin jihar ranar Litini na mako da ake ciki. Ya ce kasancewa shi shugaban NARTO a jihar ɗan uwa ne a gunsa sannan dukan…
Read More
Tashin kayan masarufi na barazanar durƙusar da kasuwanci – ‘Yan kasuwar Kano

Tashin kayan masarufi na barazanar durƙusar da kasuwanci – ‘Yan kasuwar Kano

Daga MUHAMMADU MUJJITABA a Kano Gamayyar shugabannin ƙungiyoyin 'yan kasuwar Kano da suka yi wani gangami da kira da gwamnatin Bola Tinubu sun shawarci gwamnatin Njeriya da ta ɗauki matakin gaggawa ko kuma kasuwanci ya durkushe gabaki ɗaya a Nijeriya musamman a wannan lokaci da dala ta haura Naira 1500 kuma ta ke ta hauhawar kamar motar da birkin ta ya tsinke ana gudu a 180 na ma’aunin tuƙin mota. Gamayyar ƙungiyoyin na shugabannin 'yan kasuwar Kano kimanin 30 da suka yi gangami a taron da suka gabatar a ranar Lahadi da ta gabata ƙarƙashin shugabancin shugaban gamayyar ƙungiyoyin 'yan…
Read More
Ya kamata hukuma ta kawo ƙarshen masu tallan jabun magungunan kashe ƙwari – A.A Na Mazadu

Ya kamata hukuma ta kawo ƙarshen masu tallan jabun magungunan kashe ƙwari – A.A Na Mazadu

Daga ABDULLAHI SANI DOGUWA ABKANO An sake jaddada buƙatar da ke akwai ga shuwagabannin haɗaɗiyar gamayyar masu sayar da magungunan kashe ciyayin da ke hana amfanin gona sakat da magance yawaitar yaɗuwar ƙwari masu kashe amfani, dake kasuwar Abubakar Rimi, Kano, da su yi wani abu da zai kawo ƙarshen babbar matsalar nan ta sayar da jabun magungunan kashe ƙwari , da lamarin ke neman ɓata wa 'ya'yan ƙungiyar suna. Aminu isyaku A.A na mazadu, ɗan kasuwa dake sayar da magungunan kashe ƙwari da illata amfanin gona a rukunin masu sayar da maganin kashe ƙwari a babbar kasuwar Abubakar Rimi…
Read More
Kamfanoni sun kama hanyar rage farashin siminti da kaso mai ma’ana

Kamfanoni sun kama hanyar rage farashin siminti da kaso mai ma’ana

Daga BASHIR ISAH Kamfanonin siminti a Nijeriya sun amince su saukar da farashin buhun suminti mai nauyin 50kg zuwa tsakanin N7,000 da N8,000. Kamnonin sun ce za su saukar da farashin ba da ɓata lokaci ba da zarar Gwamnatin Tarayya cika shariɗin da aka cimma a yarjejeniyar da aka yi. An cimma wannan yarjejeniya tsakanin kamfanonin da lamarin ya shafa da kuma ɓangaren gwamnati ne a wajen taron da Ministan Ayyuka, Sanata David Umahi ya shirya ranar Litinin a Abuja. Uzoka-Anite ya ce gwamnati ta ba da himma wajen ganin ta daƙile dalilan da suka haifar da tashin farashin siminti…
Read More
Ya kamata Nijeriya ta ƙara cire tallafin man fetur da na kuɗin lantarki – Bankin IMF

Ya kamata Nijeriya ta ƙara cire tallafin man fetur da na kuɗin lantarki – Bankin IMF

Daga AMINA YUSUF ALI A halin yanzu dai Bankin ba da lamunin Duniya (IMF) ya shawarci ƙasar Nijeriya da ta qara cire tallafin fetur da tallafin kuɗin lantarki. Bankin ba da Lamuni na Duniya (IMF), ya bayyana cewa, ya ba da wannan shawara ga Nijeriya na ƙara cire ɗan sauran tallafin fetur da tallafin kuɗin wutar lantarki, domin ta magance matsalolin da suka dabaibaye tattalin arzikin ƙasar. IMF ta ce barin kuɗaɗen tallafin su ne ke ƙara damalmala tattalin arzikin Nijeriya. Bankin ya ce kuma wannan matsala ta tallafi ce ke ƙara rura wutar talauci da matsalar abinci. A cikin…
Read More
Za a kafa Babban Bankin Afirka a Nijeriya

Za a kafa Babban Bankin Afirka a Nijeriya

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya bayyana cewa, a shirye Nijeriya take ta karɓi Babban Bankin Afirka bisa la'akari da ƙudirin birnin tarayya, Abuja. Tinubu ya yi wannan furuci ne sa'ilin da yake jawabi a wajen taron Ƙungiyar Ƙasashen Afirka (AU) da ke gudana a Addis Ababa, babban birnin ƙasar Habasha. Ya ƙara da cewa, gwamnatinsa za ta tattauna da dukkan waɗanda suka dace domin tabbatar da bankin ya fara aiki ya zuwa 2028 kamar yadda aka shirya. Shugaba Tinubu ya faɗa wa taron cewa, iya magance ƙalibalan Afirka na tattare ne da irin matsayar da shugabannin nahiyar…
Read More
An sake buɗe Sahad Stores a Abuja bayan shafe sa’o’i 24 a rufe

An sake buɗe Sahad Stores a Abuja bayan shafe sa’o’i 24 a rufe

Daga BASHIR ISAH Gwamnatin Tarayya ta hannun Hukumar Kula da Haƙƙin Masu Amfani da Kayayyaki (FCCPC), ta sake buɗe katafaren shagon nan na zamani, wato Sahad Stores, da ke yankin Garki a Abuja bayan rufe shi na kimanin sa’o’i 24. MANHAJA ta kalato cewar, an ga harkoki sun ci gaba da gudana a shagon yayin ziyarar da aka kai yankin a ranar Asabar. A ranar Juma’ar da ta gabata gwamnati ta garƙame shagon saboda rashin daidaito da gaskiya a farashin kayayyakinsa. Hukumar FCCPC ta bayyana a cikin sanarwar da ta fitar cewa, bincikenta ya gano farashin da ke rubuce a…
Read More