Tattaunawa

Matasan marubuta ba sa son ana musu gyara – Mukhtar Ƙwalisa

Matasan marubuta ba sa son ana musu gyara – Mukhtar Ƙwalisa

"A rubutu na yi aure, na yi muhalli na kaina" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Ga duk wani tsohon makarancin littattafan Hausa, musamman littattafan labaran yaƙe-yaƙe da na barkwanci ba zai kasa sanin littattafan marubuci Mukhtar Ƙwalisa ba, wanda ya yi suna wajen tsara labarai masu ɗaukar hankali da sanya nishaɗi a zuciyar mai karatu. A wannan makon, shafin Adabi ya gayyato muku ɗan ƙwalisar marubuta, don jin abin da ya sa har yanzu yake ci gaba da wallafa littattafai duk kuwa da kasancewar takwarorinsa da dama yanzu harkar ta gagare su. A tattaunawar da suka yi da wakilin Blueprint Manhaja,…
Read More
Wacce ta ce jari ya hana ta sana’a, ba ta tashi yi ba – Hafsat Adamu 

Wacce ta ce jari ya hana ta sana’a, ba ta tashi yi ba – Hafsat Adamu 

"Ilimin 'ya mace har mijinta ke amfana" Daga AISHA ASAS  Mai karatu barkan mu da sake ganin zagayowar sati lafiya. Kamar kowanne mako, shafin Gimbiya na yi maku tanadi na musamman wanda muke da tabbacin mata za su amfana ta vangarori da dama, ya Allah ya zama ƙwarin gwiwa ga wasu, wasu ya zama ilimi da zai taimaka masu wurin miƙewa neman na kai, yayin da yake zama allon kwaikwayo don saisaita rayuwarsu bisa ga turba da za ta tsirar da su. A wannan satin, mun samu baƙuncin wata matashiya da ta ɗauki sana'a da muhimmanci, mai sana'ar 'yankunne ce,…
Read More
Babu amfanin samun mace in har ba za ta taimaki mijinta ba – Jiddah Haulat Nguru (2)

Babu amfanin samun mace in har ba za ta taimaki mijinta ba – Jiddah Haulat Nguru (2)

"A wannan zamani sana'a kamar dole ta zamewa 'ya mace" Daga AISHA ASAS A satin da ya gabata, mai karatu idan bai manta ba, mun ɗauko fira da matashiya Jiddah Haulat Nguru, inda ta fara bayyana mana tarihi da kuma irin sana'ar da take yi, wadda ta tabbatar mana ana cin kasuwarta ne a kafafen sadarwa, sannan ta yi mana bayanin yadda ta fara, da hanyoyin da take bi don siya da siyar da kayanta a kafafe kamar Fesbuk, WhatsApp da sauransu. A wannan satin, za mu ɗora ne daga inda muka tsaya. Kamar yadda muka sanar, baƙuwar tamu za…
Read More
Matar da har yau ban san ta ba ce ta koya min yadda zan gyara rubutuna – Zee Kumurya

Matar da har yau ban san ta ba ce ta koya min yadda zan gyara rubutuna – Zee Kumurya

"Rashin haɗin kan marubta onlayin ne ya fi damuna" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU A wannan makon muna ɗauke ne da tattaunawar da wakilin Blueprint Manhaja Abba Abubakar Yakubu ya yi da marubuciya Zainab Shehu Abdullahi, wacce aka fi sani da Zee Kumurya. A cikin tattaunawar tasu za ku ji yadda ta fara samun kanta a harkar rubutun adabi, da buƙatarta na ganin an samu haɗin kai da kyakkyawan jagoranci a tsakanin marubuta. A yi karatu lafiya. MANHAJA: Ina son ki gabatar mana da kanki? ZEE KUMURYA: To, Alhamdulillahi. Cikakken sunana shi ne Zainab Shehu Abdullahi, wacce aka fi sani da…
Read More
Muna so matasa su karkato ga sana’o’in gargajiya – Sarkin Askar Jihar Filato

Muna so matasa su karkato ga sana’o’in gargajiya – Sarkin Askar Jihar Filato

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  A yayin da sana'o'in gargajiya daban-daban ke samun koma baya, saboda sauye sauyen zamani da rashin samun tallafin hukumomi. An fara ganin farfaɗowar wasu tsofaffin sana'o'in Hausawa na iyaye da kakanni da ke ƙoƙarin jawo hankalin matasa ga raya al'adunsu na gado, don samun abin dogaro. Harkar wanzanci na daga cikin waɗannan sana'o'in da daruruwan matasa ke cin abinci a cikinta, sakamakon sabbin jinin shugabanni da aka samu da ke ƙoƙarin inganta sana'ar da kuma ƙara kusantar da ƙungiyar raya harkar wanzanci ga gwamnati, don kawo wa sana'ar cigaba. Wakilin Blueprint Manhaja a Jos, ABBA ABUBAKAR…
Read More
Manufarmu ce tsamo matasa daga ƙangin talauci da aikata laifuffuka – Kwamaret Alkamatu

Manufarmu ce tsamo matasa daga ƙangin talauci da aikata laifuffuka – Kwamaret Alkamatu

Kamfanin Alkamatu Kamfani ne da ya yi fice a jahar Kano, wajen samar wa da al'umma mafita don dogaro da kai. Sannan suna samar wa da mutane bashi daga bankuna tare da tallafin kuɗaɗe don cigaba da kasuwanci don tsayawa da ƙafafunsu. Wakilin Blueprint Manhaja a Kano, Babangida S. Gora ya samu tattaunawa da Shugaban Kamfanin Alkamawa. Ga yadda tattaunawar ta kasance.  MANHAJA: Da farko za mu so mu ji da wa muke tare. ALKAMATU: Ni Sunana Alkamatu Hussaini Abdulƙadir, Kuma ni ne shugaban wannan kamfani na Alkamatu BrainBox Solutions. Mene ne manufarka ta samar da wannan kamfani? to kusan…
Read More
Henderson ya koma Al-Ettifaq ta Saudiyya

Henderson ya koma Al-Ettifaq ta Saudiyya

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Kyaftin ɗin Liverpool, Jordan Henderson ya koma Al-Ettifaq mai buga babbar gasar ƙwallon ƙafa ta Saudiyya. Ɗan ƙwallon tawagar Ingila, mai shekara 33 ya amince da ƙunshin yarjejeniyar fam miliyan 12 har da ƙarin tsarabe-tsarabe. A sakon ban kwana da ya yi wa Liverpool, ya ce zai bar ƙungiyar inda ya yi kaka 12, wadda ya lashe firimiya da Champions League a ita da sauran nasarori. Henderson yana Liverpool tun bayan da ya koma Anfield daga Sunderlandn kan fam miliyan 20 a watan Yunin 2011. Ya buga karawa 492 da cin ƙwallo 33 da bayar da…
Read More
Har yanzu ‘yan Nijeriya na fama da matsalar tsaro lokacin Tinibu – Dauda

Har yanzu ‘yan Nijeriya na fama da matsalar tsaro lokacin Tinibu – Dauda

Daga AMINU AMANAWA a Sakkwato Ƙasa da watanni biyu da soma mulkin Shugaban Ƙasa Bola Ahmad Tinibu al’umma na cigaba da bayyana damuwarsu kan kamun ludayin gwamnatin musamman a ɓangaren tsaro. A cewar galibin waɗanda Jaridar Manhaja ta zanta da su sun bayyana damuwar su, kan yadda duk da alƙawurran da gwamnatin Tinibun ta yi wa ‘yan ƙasa kan lamarin tsaro, al’umma ke cigaba da ɗanɗana kuɗar su sakamakon har-haren ‘yan bindiga musamman ma a jihohin Arewa maso Yammacin Nijeriya. Kwamared Bishir Dauda Sabon Unguwa Katsina, shi ne Babban Magatakardan Ƙungiyar Muryar Talaka a Nijeriya, a zantawar da wakilinmu a…
Read More
Muna son matasa su karkato da tunaninsu ga sana’o’in gargajiya – Sarkin Askan Jos

Muna son matasa su karkato da tunaninsu ga sana’o’in gargajiya – Sarkin Askan Jos

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU A yayin da sana'o'in gargajiya daban-daban ke samun koma baya, saboda sauye sauyen zamani da rashin samun tallafin hukumomi. An fara ganin farfaɗowar wasu tsofaffin sana'o'in Hausawa na iyaye da kakanni da ke ƙoƙarin jawo hankalin matasa ga raya al'adunsu na gado, don samun abin dogaro. Harkar wanzanci na daga cikin waɗannan sana'o'in da daruruwan matasa ke cin abinci a cikinta, sakamakon sabbin jinin shugabanni da aka samu da ke qoqarin inganta sana'ar da kuma ƙara kusantar da ƙungiyar raya harkar wanzanci ga gwamnati, don kawo wa sana'ar cigaba. Wakilin Blueprint Manhaja a Jos, ABBA ABUBAKAR…
Read More
Babu wahala ga duk wata sana’ar da ka sa kanka – Maryam Ceetar

Babu wahala ga duk wata sana’ar da ka sa kanka – Maryam Ceetar

"Tun Ina ƙarama nake da burin neman na kaina" DAGA MUKHTAR YAKUBU A daidai lokacin da a ke ganin mata an bar su a baya wajen harkar kasuwanci da sana'o'i tare da kiraye kirayen da ƙungiyoyin kare muradun mata suke yi na mata su tashi su nemi na kan su, an samu wata jaruma a cikin mata wadda ta zama kallabi tsakanin rawuna. Maryam Isah Abubakar Ceetar mace ce da take harkokin kasuwanci da sana'o'i na kanta wadda har ta kai a yanzu tana da kamfanin gine-gine da kuma qawata gidaje, baya ga harkokin kasuwanci da take yi. Ganin yadda…
Read More