Kasashen Waje

Yawan fasinjojin da aka yi jigilar su ta jiragen sama a ƙasar Sin ya kai 33.1% bisa adadin dukkan sufuri a ƙasar

Yawan fasinjojin da aka yi jigilar su ta jiragen sama a ƙasar Sin ya kai 33.1% bisa adadin dukkan sufuri a ƙasar

Daga CMG HAUSA A cikin shekaru 10 da suka gabata, an samu bunkasuwar sha’anin sufurin jiragen sama na ƙasar Sin sosai, yawan fasinjojin da aka yi jigilar su ta jiragen sama ya kai kashi 33.1 cikin ɗari bisa adadin dukkan sufurin ƙasar. Sin ta daddale yarjejeniyoyin jigilar jiragen sama tare da ƙasashe da yankuna 128, da buɗe hanyoyin jiragen sama 895 a tsakaninta da ƙasashen waje. A cikin shekaru 10 da suka gabata, an gina sabbin filayen jiragen sama ko canja wurin filayen jiragen sama 82 a ƙasar Sin, a halin yanzu yawan filayen saman ƙasar Sin ya kai 250,…
Read More
Mara wa kamfanoni ma su zaman kansu baya zai amfani ƙasar Sin da ma duniya baki ɗaya

Mara wa kamfanoni ma su zaman kansu baya zai amfani ƙasar Sin da ma duniya baki ɗaya

Daga CMG Hausa Kwanan baya shugaban ƙasar Sin Xi Jinping, ya yi rangadin aiki a lardin Sichuan dake yammacin ƙasar Sin, inda ya ziyarci wani kamfani mai zaman kansa mai suna Gimi, dake ƙera kayan laturoni, da na samar da wutar lantarki. Shugaba Xi ya shiga ɗakin nune-nune da sashin ƙere-ƙere na kamfanin, inda ya ƙara fahimtar yadda kamfanin ke gudanar da ayyukan ƙirƙire-ƙirƙire da nuna goyon-baya ga raya tattalin arzikin wurin da sauransu, al’amarin da ya sake shaida cewa, ƙasar Sin na matukar maida hankali, gami da nuna goyon-baya ga raya tattalin arziki mai zaman kansa. Sakamakon yaɗuwar annobar…
Read More
Jakadan Sin a Saliyo ya halarci taron ƙarawa juna sani tsakanin ofishin jakadancinsa da ƙungiyoyin sada zumunta ta ƙasashen biyu

Jakadan Sin a Saliyo ya halarci taron ƙarawa juna sani tsakanin ofishin jakadancinsa da ƙungiyoyin sada zumunta ta ƙasashen biyu

Daga CMG HAUSA A ranar 8 ga wata, ofishin jakadancin ƙasar Sin dake Saliyo, ya shirya taron ƙarawa juna sani tsakanin ofishin da ƙungiyoyin sada zumunta ta ƙasashen Sin da Saliyo na shekarar 2022. Jakadan ƙasar Sin a Saliyo, Hu Zhangliang, ya gabatar da muhimmin jawabi game da halin da ƙasa da ƙasa ke ciki a halin yanzu, da manufofin bunƙasa cigaba na ƙasar Sin da na diflomasiyyarta, da kuma hulɗar dake tsakanin Sin da Saliyo. Ya bayyana cewa, ƙasar Sin ta ƙara ƙaimi tare da samar da gagarumin taimako ga zaman lafiya da cigaban duniya. Yadda ƙasar da ke…
Read More
Me aka tattauna a wajen shawarwarin ministocin tsaron Sin da Amurka?

Me aka tattauna a wajen shawarwarin ministocin tsaron Sin da Amurka?

Daga CMG HAUSA Jiya Jumma’a 10 ga wata, mai magana da yawun ma’aikatar tsaron ƙasar Sin, Wu Qian, ya kira taron manema labarai a wajen shawarwarin Shangri-La ko kuma SLD a taƙaice a ƙasar Singapore, inda ya bayyana yadda aka gudanar da shawarwarin ministocin tsaron ƙasashen Sin da Amurka. Wu ya ce, a yayin shawarwarin, ministan tsaron ƙasar Sin, Wei Fenghe, ya jaddada matsayin ƙasar Sin kan batun Taiwan, inda ya ce, Sin ƙasa ce daya tilo a duniya, kuma Taiwan wani yanki ne da ba za’a iya balle shi daga ƙasar Sin ba. Manufar kasancewar ƙasar Sin ɗaya tilo…
Read More
Rahoton ƙarya da Adrian Zenz ya watsa ya tona asirin Amurka

Rahoton ƙarya da Adrian Zenz ya watsa ya tona asirin Amurka

Daga CMG HAUSA Wata doka mai suna wai hana tilastawa ‘yan Uygur aiki ta Amurka za ta fara aiki nan bada jimawa ba. Kwanan nan, Adrian Zenz, wanda ya sha kitsa ƙarairayi ya sake fitar da wani rahoton dake nuna cewa, wai ƙasar Sin na ƙara tilasta wa mutane aiki. Irin wannan doka tana cike da ƙarairayi, wadda ta tona asirin kasar Amurka, na kawar da Xinjiang daga cikin yankuna masu samar da kayayyaki ga duniya. Haƙiƙa, kafofin watsa labarai sun ruwaito maganganun tsoffin ‘yan diflomasiyyar Amurka a ƙasar Sin dake cewa, babu wata matsala a Xinjiang, dukkanmu mun sani,…
Read More
Ƙasar Sin ta nuna adawa da ƙudurin Majalisar Turai kan Xinjiang

Ƙasar Sin ta nuna adawa da ƙudurin Majalisar Turai kan Xinjiang

Daga CMG HAUSA Mai magana da yawun majalisar dokokin ƙasar Sin ya bayyana adawa da kakkausar murya kan wani sabon ƙuduri da majalisar Turai ta amince da shi, kan halin da ake ciki game da batun kare haƙƙin dan-Adam a jihar Xinjiang. Kakakin kwamitin kula da harkokin waje na majalisar wakilan jama'ar Ƙasar Sin You Wenze ya bayyana cewa, ƙasar Sin tana adawa da magudin siyasa da tsoma baki a harkokin cikin gidan ta da majalisar Turai ke yi, ta hanyar fakewa da batun kare haƙƙin bil-Adama Manufar yunƙurin da wasu makiya ƙasar Sin dake cikin majalisar dokokin Turai ke…
Read More
Sin: Kimiyya da fasaha sun taimakawa wajen bunƙasar kamfanoni da horas da ƙwararru

Sin: Kimiyya da fasaha sun taimakawa wajen bunƙasar kamfanoni da horas da ƙwararru

Daga CMG HAUSA A shekaru 10 da suka wuce, kamfanoni da sauran masu dandalin kasuwanci suna ta kara ƙarfin zuba jari a fannin kimiyya da fasaha, lamarin da ya taimaka wajen horas da dimbin ƙwararru. Alƙaluma sun nuna cewa, yanzu yawan kuɗin da kamfanoni suke zubawa a fannin nazari ya wuce kashi 76 bisa 100 na jimillar kuɗin da zamantakewar al’ummar ƙasar Sin suke zubawa. Kana gwamnatin tsakiyar ƙasar Sin ta fito da manufofi da matakai da dama don ƙarfafa gwiwar kamfanoni da su ƙara zuba kuɗi kan aikin nazari, a ƙoƙarin kyautata ƙwarewarsu ta fannin yin ƙirƙire-ƙirƙire. Yanzu haka…
Read More
Da abokin daka akan sha gari

Da abokin daka akan sha gari

Daga SAMINU HASSAN Kamar yadda muke ji yau da kullum daga bakin masana, cewa babu wata ƙasa a duniyar nan da za ta samu cikakken ci gaba, ba tare da bunƙasa yankunanta na karkara ba, muna iya ganin shaidu na zahiri don gane da hakan a nan ƙasar Sin. Mahukuntan ƙasar Sin sun jima da fahimtar muhimmancin kawar da ƙangin talauci da raya karkara, a matsayin babban jigon gina ƙasa, tare da tabbatar da ba a bar wani ɓangare na alummar Sinawa a baya ba. Kaza lika da yake yankunan karkara na taka muhimmiyar rawa wajen gina ƙasa, ta hanyar…
Read More
Xi Jinping ya rubuta wasiƙa ga mahalarta taron ƙarawa juna sani na jam’iyyu shida dake Kudancin Afirka da suka kafa makarantar Julius Nyerere

Xi Jinping ya rubuta wasiƙa ga mahalarta taron ƙarawa juna sani na jam’iyyu shida dake Kudancin Afirka da suka kafa makarantar Julius Nyerere

Daga CMG HAUSA Jiya Laraba, shugaban ƙasar Sin Xi Jinping, ya rubuta sako ga dukkan mahalarta taron sanin makamar aiki na jami’ai matasa na jam’iyyu shida dake kudancin nahiyar Afirka, waɗanda suka kafa makarantar koyar da harkokin shugabanci ta Julius Nyerere. Xi ya ce, neman cimma muradun ci gaba, da farfaɗo da al’umma da samar da alfanu ga jama’a, na buƙatar jajircewar zuriyoyin al’umma. Kara gina duniya mai kyakkyawar makoma, na buƙatar mu’amalar ƙasa da ƙasa. Xi ya jaddada fatansa cewa, ya dace waɗannan jami’an su dauki nauyin dake wuyansu, da nuna kwazo wajen raya sha’anin ƙarfafa zumunta tsakanin Sin…
Read More
Sin ta yi kira da a kiyaye zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin Tsakiyar Afirka

Sin ta yi kira da a kiyaye zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin Tsakiyar Afirka

Daga CMG HAUSA Dai Bing, mataimakin zaunannen wakilin ƙasar Sin a MƊD ya yi kira da a kiyaye zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin tsakiyar Afirka. Dai Bing ya faɗi haka ne yayin wani taron kwamitin sulhu na MƊD kan batun yankin tsakiyar Afirka da aka yi a jiya, inda ya kuma nuna cewa, tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin na tsakiyar Afirka, yana amfanawa cikakken tsaron nahiyar Afirka. Kuma ƙasar Sin na tsayawa tsayin daka wajen goyon bayan ƙasashen da ke yankin da su yi ƙoƙarin kiyaye ikon mulkin ƙasa da cikakkun yankunansu. Ya ce…
Read More