Labarai

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mutum 87 a wani sabon hari a Kaduna

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mutum 87 a wani sabon hari a Kaduna

Daga BASHIR ISAH 'Yan bindiga a Jihar Kaduna sun yi garkuwa da mutum 87 a wani sabon harin da suka kai yankin Tashar Kajuru da ke jihar. Wani matashi a yankin mai suna Harisu Dari, shi ne ya tabbatar da aukuwar hakan ga majiyarmu a ranar Litinin. Wannan na zuwa ne bayan wasu 'yan kwanaki da 'yan bindigar suka hari a yankin Dogon Noma da kuma kauyen Kuriga inda suka sace ɗailiban firamare su sama da 200. Bayanai sun ce, maharan sun kuma fasa shaguna inda suka kwashi kayayyaki da dama yayin harin. Yawan hare-haren ta'addancin da ke aukuwa a…
Read More
Gobara ta laƙume wani sashen Babbar Kasuwar Sakkwato

Gobara ta laƙume wani sashen Babbar Kasuwar Sakkwato

Daga BASHIR ISAH Rahotanni da muka samu daga jihar Sakkwato na nuni da cewa, an samu aukuwar gobara a Babbar Kasuwar Sakkwato. Bayanai sun ce gobarar ta fi ƙamari a sashen masu sayar da bababura a kasuwar. Duk da dai babu cikakken bayani kan dalilin aukuwar gobarar, sai dai MANHAJA ta tattaro cewar da safiyar ranar Litinin iftila'in ya auku. Shugaban Ƙungiyar Masu Sayar da Babura a Kasuwar, Shehu Muhammad, ya ce ba a kai ga gano adadin ɓarnar da gobarar ta yi ba saboda rashin tsagaitawar wutar. An ga jami'an kashe gobada na jiha da na tarayya a wurin…
Read More
‘Yan bindiga a Bauchi sun kashe basarake sa’o’i 24 bayan sun yi garkuwa da shi

‘Yan bindiga a Bauchi sun kashe basarake sa’o’i 24 bayan sun yi garkuwa da shi

Daga BASHIR ISAH 'Yan bindiga a Jihar Bauchi sun kashe Dagacin ƙauyen Riruwai, Alhaji Garba Bafamasi, da ke yankin Ƙaramar Hukumar Toro a jihar. MANHAJA ta kalato cewar, 'yan ta'addan sun kashe basaraken ne sa'o'i 24 bayan da suka yi garkuwa da shi. Rahotanni sun ce a ranar Juma'a, 15 ga Maris, 'yan bindigar suka dira fadar Alhaji Badamasi inda suka razanar da jama'ar yankin da harbin bindiga kafin daga bisani suka yi awon gaba da shi. Majaiyarmu ta ce, 'yan bindigar ba su damu da kiran 'yan basaraken don neman fansa ba, lamarin da ya sa aka kasa gane…
Read More
Hedikwatar Tsaro na shirin fitar da sunayen ‘yan ta’addan da take nema ruwa a jallo

Hedikwatar Tsaro na shirin fitar da sunayen ‘yan ta’addan da take nema ruwa a jallo

Daga BASHIR ISAH Alamu na nuni da cewa nan ba da daɗewa ba, Babban Ofishin Tsaro zai saki sunaye da hotunan kwamandojin 'yan fashin dajin da ake nema ruwa a jallo a sassan Nijeriya. Majiyarmu ta tattaro cewar, rundunar soji ta ɗauki matakin yin haka ne biyo bayan bayyanar wasu sabbin shugabannin 'yan ta'addan sakamakon kakkaɓe na da da aka yi. Idan za a iya tunawa, a watan Nuwamban 2022 Babban Ofishin Tsaro ya sanar kan cewa yana neman wasu kwamandojin 'yan ta'addan aƙalla su 19 ruwa a jallo, tare da sanya tukwicin Naira milyan 5 a kan kowannensu ga…
Read More
Allah Ya yi wa Sheikh Surajo Rabi’ah rasuwa

Allah Ya yi wa Sheikh Surajo Rabi’ah rasuwa

Daga BASHIR ISAH Allah Ya yi wa fitaccen malamin nan, Sheikh Surajo Rabi'ah, rasuwa a Gusau, babban Jihar Zamfara. Da ƙarfe 6 na yammacin Lahadi ake sa ran za a yi jana'izar marigayin a Masallacin Rabi'ah, inda jama'a za su haɗu don gabatar da sallar janaza. Kawo yanzu, jama'a da dama kuma daga sassa daban-daban ke ci gaba da miƙa saƙonnin ta'aziyya tare da taya 'yan marigayin alhinin wannan rashi. A halin rayuwarsa, marigayin ya yi fice wajen yin da'awa ƙarƙashin Ƙungiyar Izalatul Bidi'a Wa Iƙamatus Sunna.
Read More
Maraba da watan Ramadana mai albarka!

Maraba da watan Ramadana mai albarka!

Kamar yadda aka sani ne, Allah ya kawo mu watan Ramadana mai albarka, wanda a cikinsa ake gudanar da ibadu masu ninkin lada, waɗanda idan mutum ya aikata su zai kasance yana da lada mai tarin yawan da ya fi waɗanda ya yi in ba a watan ba ne, kamar dai yadda malamai masana ba su ƙasa a gwiwa ba a duk lokacin da watan shigo. Shi watan Ramadan wata ne wanda Allah ya wajabta a yi azumi a cikinsa, sannan aka wajabta wasu abubuwa da dama, aka kuma haramta wasu abubuwan da ba haramun ba ne a watan da…
Read More
Gwamnatin Tarayya ta keɓe Dala Biliyan 1.3 don aikin dogo daga Kano zuwa Nijar

Gwamnatin Tarayya ta keɓe Dala Biliyan 1.3 don aikin dogo daga Kano zuwa Nijar

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ministan Sufuri, Said Alkali, ya sanar da wani gagarumin cigaba a fannin samar da kuɗaɗen aikin titin jirgin ƙasa daga Kano-Katsina-Jibiya-Maradi, inda aka samu dala biliyan 1.3 don gudanar da wannan shiri. A wata sanarwa da mataimaki na musamman kan harkokin jama’a na ministan, Jamilu Ja’afar ya fitar, an yaba da wannan nasarar a matsayin wani muhimmin mataki na inganta alaƙar zamantakewa da tattalin arziki tsakanin Nijeriya da Jamhuriyar Nijar. “Dala biliyan 1.3 da aka samu na aikin layin dogo na Kano-Katsina-Jibiya-Maradi babban nasara ne,” inji Alkali. Manajan daraktan hukumar kula da zirga-zirgar jiragen ƙasa ta…
Read More
Wasu ’yan mata sun ƙirƙiro janareta mai amfani da fitsari a Nijeriya

Wasu ’yan mata sun ƙirƙiro janareta mai amfani da fitsari a Nijeriya

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Wasu matasa huɗu, Duro-Aina Adebola Akindele Abiola, Faleke Oluwatoyin, da Bello Eniola, daga Legas a Nijeriya sun ƙirƙiro janareta mai amfani da fitsari wanda zai iya samar da wutar lantarki. Duro-Aina Adebola, wata matashiya ‘yar shekara 14, ta ce manufar yin amfani da fitsari wajen samar da wutar lantarki ta faro ne a lokacin da ta karanta wani labari game da wani iyali mai mutane biyar da suka rasa rayukansu sakamakon gubar 'carbon monoxide' da suka shaqi hayaqin da ke fitowa a gidan ta janareta lokacin barci. Ta ce lamarin ya dame ta tana…
Read More
An kashe sojoji 15 a Delta – Hedikwatar Tsaro

An kashe sojoji 15 a Delta – Hedikwatar Tsaro

Daga BASHIR ISAH Babban Ofishin Tsaro da ke Abuja ya bayyana cewa, jami'ansu 15 sun rasa rayukansu sakamakon rikicin ƙabilanci a Jihar Delta. A cewar ofishin, jami'an da aka kashe sun haɗa da masu muƙamin Manjo 2, Kyaftin 1, sai kuma ƙananan sojoji 12. Ya ƙara da cewa, marigayan sun cimma ajali ne yayin da suka je kwantar da tarzoma na rikicin da ya ɓarke tsakanin ƙauyukan Okuama da Okoloba da ke jihar a ranar Alhamis da ta gabata. Sanarwar manema labarai mai ɗauke da sa hannun Daraktan Yaɗa Labarai na rundudunar, Brig. Gen. Tukur Gusau, wadda aka fitar a…
Read More
Ƙarancin abinci: CBN ya bada tallafin taki buhu miliyan 2.15 domin raba wa manoma a Nijeriya

Ƙarancin abinci: CBN ya bada tallafin taki buhu miliyan 2.15 domin raba wa manoma a Nijeriya

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Ma’aikatar noma da wadatuwar abinci ta karɓi buhunan takin zamani guda miliyan 2.15 daga Babban Bankin Nijeriya, CBN. Za a raba takin ne ga manoma domin daƙile hauhawar farashin kayayyakin abinci a ƙasar tare da bunƙasa samar da abinci da kuma wadatarsa. Abubakar Kyari, ministan noma da wadatuwar abinci wanda ya yi jawabi a wajen taro a ranar Laraba a Abuja, ya nuna godiya ga Shugaban Ƙasa Bola Tinubu da CBN bisa wannan karimcin. Kyari ya tabbatar wa Gwamnan CBN, Olayemi Cardoso, cewa za a yi amfani da kayan cikin adalci tare da kai…
Read More