Labarai

INEC ta za fara ba da katin zaɓe na dindindin

INEC ta za fara ba da katin zaɓe na dindindin

Daga MAHDI M. MUUHAMMAD Hukumar Zaɓe mai Zaman Kanta ta Ƙasa INEC, ta sanar da ranar fara ba da katin zaɓe na dindindin tare da ƙara gargaɗar masu karya dokokin zaɓe gabanin zaɓen 2023. Hakan na ƙunshe a cikin wata sanarwa da shugaban kwamitin yaɗa labarai da wayar da kan masu zave na hukumar na ƙasa, Festus Okoye Esq, ya fitar da ranar Asabar a Abuja. Hukumar ta yi zamanta ne a ranar Asabar 26 ga watan Nuwamba, 2022, inda ta tattauna kan batutuwa da dama da suka haɗa da kwanan wata da tsarin karɓar katin zaɓe na dindindin (PVC)…
Read More
A hau jirgin ƙasan Abuja zuwa Kaduna gaba-gaɗi, ba fargaba, inji Ministan Sufuri

A hau jirgin ƙasan Abuja zuwa Kaduna gaba-gaɗi, ba fargaba, inji Ministan Sufuri

Daga NASIR S. GWANGWAZO a Abuja Ministan Sufurin Nijeriya, Mu'azu Jaji Sambo, ya yi kira ga 'yan Nijeriya masu sha'awar hawa jirgin ƙasa daga Abuja zuwa Kaduna da su yi shirin hawa gaba-gaɗi ba tare da wata fargaba ba, yana mai cewa, an yi kyakkyawan tanadi, don kare rayuka da lafiyar fasinjoji a yayin da zirga-zirgar jingin ta dawo. Ministan ya bayyana hakan ne lokacin da yake ganawa da manema labarai a yau Lahadi, ciki har da Blueprint Manhaja, yayin duba irin shirin da Gwamnatin Tarayya ta yi na sake buɗe zirga-zirgar jiragen ƙasa daga Abuja zuwa Kaduna. "Ina so…
Read More
DA ƊUMI-ƊUMI: Sai da Lambar ‘Yan Ƙasa za a riƙa hawa jirgin ƙasan Abuja zuwa Kaduna

DA ƊUMI-ƊUMI: Sai da Lambar ‘Yan Ƙasa za a riƙa hawa jirgin ƙasan Abuja zuwa Kaduna

Daga NASIR S. GWANGWAZO a Abuja Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta sanar da samar da tsarin yin amfani da Lambar 'Yan Ƙasa (NIN) ga kowane fasinja dake sha'awar hawa jirgin Abuja zuwa Kaduna. Ministan Sufuri na Nijeriya, Mu'azu Jaji Sambo, ne ya bayyana hakan a yau Lahadi lokacin da ya ke zagayawa da 'yan jarida, ciki har da Blueprint Manhaja, don duba irin shirye-shiryen da aka yi, don dawo da zirga-zirgar, wacce aka dakatar da ita ranar 28 ga Maris, 2022, sakamakon harin ta'addanci da aka kai masa har aka kashe wasu fasinjoji kuma aka yi awon gaba da wasu. Ministan…
Read More
Ganduje ya sa hannu kan dokar inganta rayuwar nakasassu

Ganduje ya sa hannu kan dokar inganta rayuwar nakasassu

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje ya sanya hannu a kan dokar inganta rayuwar masu buƙata ta musamman, wadda majalisar dokokin jihar ta zartar kwanan nan. Gwamnan ya ce dokar za ta taimaka wajen sanya masu larurar nakasa a cikin tsare-tsaren gwamnati da suka shafi cigaban ƙasa. Gwamna Abdullahi Umar Ganduje na jihar Kano ya ce wanzuwar wannan doka ta inganta rayuwar masu larurar nakasa za ta ba da damar fito da wannan ɓangare na al'umma da nau’o’in buƙatunsu ta yadda za a shigar da su a cikin tsarin gwamnati, tare da share musu hawaye.…
Read More
Gwamnatin Kaduna ta ƙaddamar da rajistar masu aikata fyaɗe ta fasahar zamani

Gwamnatin Kaduna ta ƙaddamar da rajistar masu aikata fyaɗe ta fasahar zamani

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Gwamnatin Jihar Kaduna ta ƙaddamar da rijistar masu aikata laifuka ta fasahar zamani ‘dijital’ a ƙoƙarinta na daƙile matsalar fyaɗe a jihar. Mataimakiyar gwamna, Dakta Hadiza Balarabe, ta ƙaddamar da rijistar dijital ɗin a ma’aikatar shari’a ta jihar, a wani taron da ya samu halartar manyan jami’an gwamnati, shugabannin hukumomin tsaro da sauran masu ruwa da tsaki a jihar. A nata jawabin, Dakta Balarabe ta ce, a cikin watan Satumba na 2020, Gwamna Nasir El-Rufai ya sanya hannu kan dokar hukunta masu fyaɗe da kuma yi wa waɗanda aka samu da laifin yi wa yara ’yan…
Read More
An kama matashi bayan yin kalamai a kan Aisha Buhari a soshiyal midiya

An kama matashi bayan yin kalamai a kan Aisha Buhari a soshiyal midiya

Daga BASHIR ISAH Jami'an tsaro sun cika hannu da wani matashi kuma ɗalibi a Jaimi'ar Tarayya da ke Dutse, kan wasu kalamai da ya yi a soshiyal midiya game da matar Shugaban Ƙasa, Aisha Buhari. A cewar rahotanni, a watan Yunin 2022 Aminu Adamu Muhammed ya wallafa wasu kalamai a shafinsa na Tiwita, inda ya nuna Aisha Buhari ta bunƙasa bayan ta ɗanɗani dukiyar ƙasa, alhali ga talakawa na fama a ƙarƙashin gwamnatin maigidanta. “Su mama an ci kuɗin talkawa an ƙoshi," waɗannan su ne kalaman da aka ce Muhammed ya wallafa a shafin nasa. Wani abokin matashin ya ce,…
Read More
An damke ɗan shekara 12 da ya yi garkuwa da ‘yar shekara uku a Bauchi

An damke ɗan shekara 12 da ya yi garkuwa da ‘yar shekara uku a Bauchi

Daga BASHIR ISAH 'Yan Sanda a Jihar Bauchi sun damke wani yaro ɗan shekara 12 a yankin Magama Gumau kan zargin yin garkuwa da wata yarinya 'yar shekara 3. Bayanan da 'yan sandan suka samu sun nuna, a ranar 23 ga Nuwamban 2022, wani mai shago da ke yankin, Yahaya Sale, ya samu kiran waya a kan ana bukatar kuɗi N150,000 daga hannunsa kafin a sako 'yarsa 'yar shekara 3 da aka yi garkuwa da ita a yankin. Binciken 'yan sanda ya gano yaron ya yaudari yarinyar zuwa wani kangon gini ne sannan ya kira mahaifin yarinyar a waya a…
Read More
Tsohon ɗan jarida, Bashir Mohammed ya rasu

Tsohon ɗan jarida, Bashir Mohammed ya rasu

Daga WAKILINMU Tsohon ɗan jaridar nan kuma mai fashin baƙi kan al'amuran yau da kullum, Bashir Mohammed Baba ya rasu. A ranar Asabar Allah Ya yi masa cikawa a wani asibitin Abuja bayan fama sa raunin da ya ji sakamakon hatsarin da ya same shi a ban-ɗaki. A halin rayuwarsa, marigayin ya kasance ƙwararren ɗan jarida kuma mai sharhi kan al'amura a manyan kafafen yaɗa labarai da suka haɗa da NTA da BBC da VOA da DW da Rediyon Prestige da ke Minna da sauransu. An jiyo da kuma ganinsa a cikin manyan shirye-shiye a gidajen talabijin da rediyo da…
Read More
Ranar Litinin jirgin ƙasan Abuja-Kaduna zai dawo da aiki – Gwamnati

Ranar Litinin jirgin ƙasan Abuja-Kaduna zai dawo da aiki – Gwamnati

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Gwamnatin Tarayya ta sanar da Litinin mai zuwa a matsayin ranar da za a dawo da zirga-zirgar jirgin ƙasan Abuja zuwa Kaduna. Kakakin Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Ƙasa ta Nijeriya (NRC), Yakub Mahmoud ne ya tabbatar da hakan ga manema labarai a ranar Asabar. Ya ce, gabanin dawo da sufurin a ranar ta Litinin, hukumar za ta fitar da cikakkun bayanai ga jama’a ranar Lahadi. Idan za a iya tunawa, a kwanakin baya ne Ministan Sufurin Jiragen Ƙasa na Nijeriya, Mu’azu Jaji Sambo, ya sanar da cewa kafin ƙarshen watan Nuwamban 2022 za a dawo…
Read More
Alhaji MK Ahmed ya kwanta dama

Alhaji MK Ahmed ya kwanta dama

Daga WAKILINMU Allah Ya yi wa Sarkin Yaƙin Lokoja, Alhaji MK Ahmed (MFR), rasuwa. Marigayin wanda tsohon sakatare ne ga marigayi Malam Aminu Kano, ya rasu ne da safiyar Asabar bayan fama da rashin lafiya. Jaridar Prime Time ta rawaito cewa, marigayin ya bar duniya yana da shekara 89. Ya rasu ya bar 'ya'ya da dama, ciki har da Barista Naseer Ahmed, mamallakin fitaccen Otale ɗin Grand Central da ke Kano.
Read More