01
Dec
Daga MAHDI M. MUHAMMAD Babbar Kotun Birnin Tarayya Abuja mai lamba 14, ta tura wani ɗalibin Jami’ar Tarayya da ke Dutse a Jihar Jigawa, Aminu Mohammed zuwa gidan gyaran hali na Suleja da ke Jihar Neja bisa zargin rubutun cin zarafin Uwargidan Shugaban Ƙasa, Aisha Buhari a shafinsa na Tuwita. An gurfanar da ɗalibin ne a Abuja a ranar Talata 29 ga watan Nuwamba, 2022 bisa laifin zamba ta yanar gizo inda aka hana belinsa duk da cewa ya ƙi amsa laifin da ake tuhumarsa da shi. Idan ba a manta ba, Blueprint Manhaja ta ruwaito cewa, jami’an tsaro ne…