Labarai

NDLEA ta kama bindigogi 27 a Neja

NDLEA ta kama bindigogi 27 a Neja

Daga AISHA ASAS Jami'an Hukumar Yaƙi da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi (NDLEA) a jihar Neja, sun kama wasu mutum biyu ɗauke da bindigogi 27 yayin da suke bakin aiki na bincike abubuwan hawa a yankin Kontagora. Waɗanda ake zargin, Danjuma Auta ɗan shekara 35, da Daniel Danrangi mai shekara 25, dukkansu 'yan asalin Dirin Daji ne a yankin Ƙaramar Hukumar Sakaba, jihar Kebbi, sun faɗa a hannun jami'an ne a hanyar Kontagora zuwa Zuru a Litinin da ta gabata da daddare. A cewar Kwamandan Hukumar na jihar Neja, Mr. Aloye Isaac Oludare, an kama su biyun ɗauke da bindigogi AK 47…
Read More
Buhari ya hana jiragen sama shawagi a Zamfara

Buhari ya hana jiragen sama shawagi a Zamfara

Daga FATUHU MUSTAPHA Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya bayyana dokar hana jiragen sama shawagi a Zamfara tare da haramta duka ayyukan haƙar ma'dinai a jihar. Mai bai wa Buhari shawara kan harkokin tsaro, Major General Babagana Monguno (mai murabus) ne ya bayyana haka a ranar Talata a Abuja. Inda ya ce an ɗauki matakin haka ne domin kawar da matsalolin tsaron da ake fuskanta a jihar. Monguno ya bayyana wa manema labarai haka ne jim kaɗan bayan kammala taron Majalisar Tsaro ta Ƙasa wanda ya gudana a Fadar Shugaban Ƙasa ƙarƙashin jagorancin Shugaba Buhari. Wannan mataki na haramta wa jiragen…
Read More
Sarkin Kagara ya rasu

Sarkin Kagara ya rasu

Daga BASHIR ISAH Allah Ya yi wa Sarkin Kagara, Alhaji Salihu Tanko, rasuwa. Tuni dai Gwamnan Neja, Abubakar Sani Bello ya yi jajantawa ga Etsu Nupe kuma Shugaban Majalisar Sarakunan Neja, Alhaji Yahaya Abubakar, iyalai da ma ɗaukacin al'ummar Masarautar Kagara dangane da rasuwar. Bello, ya yi addu'ar Allah Ya jiƙan marigayin da rahma, Ya sanya Aljanna makomarsa, kana ya bai wa iyalansa haƙuri da juriyar rashin. Marigayin ya rasu ne a wannan Talatar, a garin Kagara, hedikwatar Ƙaramar Hukumar Rafi. An haife shi ne a ran 5 ga Afrilun 1930 a Tegina. Ya rasu ya bar 'ya'ya, mata da…
Read More
Nijeriya ta samu ƙarin mutum 240 da suka harbu da cutar korona

Nijeriya ta samu ƙarin mutum 240 da suka harbu da cutar korona

Daga WAKILINMU An bada sanarwar cewa Nijetiya ta samu ƙarin wasu mutum 240 da suka kamu da cutar korona a 'yan sa'o'in da suka gabata. Cibiyar Yaƙi da Yaɗuwar Cututtuka ta Kasa (NCDC) ce ta bada sanarwar haka da daddare a Lahadin da ta gabata, ta shafinta na twita. Ƙarin da NCDC ta ce an samu ya shafi wasu jihohi ne su 13 kamar haka: Anambra 85, Lagos 82, Osun 17, Ogun 10, Kwara 9, FCT 8, Kano 7, Abia 6, Ekiti5, Borno 4, Edo 2, Bayelsa 2, Kaduna 2 da kuma Rivers 1. Cibiyar ta ce katafariyar cibiyar bada…
Read More
Minista Bello ya ƙaddamar da shirin kiyaye dokokin hanyoyi a Abuja

Minista Bello ya ƙaddamar da shirin kiyaye dokokin hanyoyi a Abuja

Daga AISHA ASAS Ministan Abuja Malam Muhammad Musa Bello, ya ƙaddamar da shirin yaƙi da karya dokokin hanya a birnin Abuja a matsayin wani mataki na tabbatar da jama'a na kiyaye dokokin hanya yadda ya kamata a cikin birnin. Ƙaddamar da shirin ya auku ne a ƙarshen makon da ya gabata a Abuja. A lokacin da yake jawabi a wajen taron ƙaddamarwar, Bello ya tunatar da mazauna Abuja cewa dukkanin ƙa'idoji da alamomin da aka sanya a hanyoyi, an yi hakan ne da nufin kare rayukan masu amfani da hanyoyin da kuma hana cunkoso. Yana mai cewa, duba da yadda…
Read More
Za mu yi maganin ‘yan fashi da masu tada ƙayar-baya, cewar Buhari

Za mu yi maganin ‘yan fashi da masu tada ƙayar-baya, cewar Buhari

Daga FATUHU MUSTAPHA Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, yayi gargaɗin cewa babu wani sassauci game da matakan da gwamnati ta shirya ɗauka na neman kawar da matsalolin 'yan fashi da masu tada ƙayar-baya da sauran manyan laifuka da suka addabi al'umma a faɗin ƙasa. Buhari ya yi wannan gargaɗi ne ta bakin Shugaban Ma'aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Farfesa Ibrahim Gambari, yayin wani taro kan sha'anin tsaro wanda gwamnonin Arewa da sarakunan gargajiya suka gudanar a Jihar Kaduna. Buhari ya yarda cewa lallai Nijeriya na fama da matsalolin tsaro, amma cewa ya buƙaci sabbin shugabannin tsaro da samar da sabbin dabaru kuma…
Read More
EFCC ta yi sabon shugaba

EFCC ta yi sabon shugaba

Daga FATUHU MUSTAPHA A Larabar da ta gabata Majalisar Dattawan Nijeriya ta tabbatar da Abdulrasheed Bawa a matsayin sabon Shugaban Hukumar Yaƙi da yi wa Tattalin Arziki Zagon Ƙasa da Zambar Kuɗaɗe (EFCC). Sanatocin sun shafe sa’o’i biyu suna tantance Bawa kafin daga bisani suka tabbatar da shi a sabon matsayin nasa. Yayin da ake tantance shi, Bawa ya bai wa majalisar tabbacin cewa zai yi aiki tukuru don gyara wa hukumar zama ta hanyar inganta harkokinta kafin ƙarewar wa’adin jagorancinsa. Bawa ya ce zai yi aiki tare da waɗanda suka dace a sassan duniya domin tabbatar da Nijeriya ta…
Read More
Bello ya rattaba hannu a wasu sabbin dokokin jiharsa

Bello ya rattaba hannu a wasu sabbin dokokin jiharsa

Daga AISHA ASAS Gwamnan jihar Neja, Abubakar Sani Bello, ya sanya wa wasu sabbin dokoki guda biyu hannu. Dokokin su ne, dokar gudanar da binciken sanin lafiyar masu shirin yin aure kafin ƙulla aure da kuma dokar haramta tada hankalin jama'a da abin da ya jiɓanci haka. Taron sanya wa dokokin hannu ya gudana ne a Fadar Gwamnatin Jihar da ke Minna. Da yake jawabi bayan kammala sanya wa dokokin hannu, Gwama Bello ya bayyana dokokin a matsayin masu muhimmancin gaske. Bello ya yaba wa Majalisar Dokokin jihar bisa ƙoƙarin da ta yi wajen nazarin dokokin yadda ya dace har…
Read More
An yi garkuwa da sirikar Mangal a Katsina

An yi garkuwa da sirikar Mangal a Katsina

Daga FATUHU MUSTAPHA Rahotannin da Manhaja ta samu daga jihar Katsina, sun nuna 'yan bindiga sun sace sirikar hamshaƙin ɗan kasuwar nan Alhaji Dahiru Barau Mangal, a Katsina. Majiyar Manhaja ta ce lamarin ya faru ne a daren Talata a yankin ƙaramar hukumar Matazu, inda 'yan bindigar suka je suka ɗauki Hajiya Rabi. Majiyar wadda ta buƙaci a sakaya sunanta, ta ce da misalin karfe 1 na daren Talata 'yan bindigar suka shiga gari suka tafi kai tsaye zuwa gidan Hajiya Rabi suka ɗauke ta suka yi gaba ba tare da an san inda suka nufa ba. Da ma dai…
Read More
EFCC ta kama ‘yan fashin intanet 9 a Minna

EFCC ta kama ‘yan fashin intanet 9 a Minna

Daga BASHIR ISAH Hukumar Yaƙi da yi wa Tattalin Arziki Zagon Ƙasa da Zambar Kuɗaɗe (EFCC), ta cafke wasu 'yan fashin intanet su tara a Minna, babban birnin jihar Neja. EFCC ta cafke waɗanda lamarin ya shafa ne a ranar Litinin biyo bayan bayanan sirri da ta ce ta samu a kansu dangane da ayyukan zambatar mutane da suke aikatawa. Kayayyakin da EFCC ta ce ta ƙwace a hannu matasan sun haɗa da ƙananan kwamfutoci da wayoyin salula da kuma motoci. Hukumar ta ce, za ta gurfanar da 'yan fashin a kotu da zarar ta kammala bincikenta.
Read More