17
Feb
Daga AISHA ASAS Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya ɗora alhakin faruwar wasu rikice-rikice a sassan ƙasar nan kan attajirai da masu matsayi, tare da shan alwashin yin maganinsu. Buhari ya yi wannan magana ne a ranar Talata a lokacin da ya karɓi baƙuncin tawagar dattawan Barno da Yobe a fadarsa da ke Abuja kamar dai yadda mai ba shi shawara kan harkokin yaɗa labarai, Femi Adesina ya bayyana. A sanarwar da Femi ya fitar Buhari ya ce, "Muna da buƙatar wannan ƙasa, za mu ci gaba da aiki domin samun daidaito. "Ina da yaƙinin cewa za mu shawo kan 'yan…