Babban Labari

Buhari da Tinubu: Ta faru ta ƙare!

Buhari da Tinubu: Ta faru ta ƙare!

*Yayin da Tinubu ya kammala shirin amsar mulki…*Buhari ya yi sabbin naɗe-naɗe 33 kwanaki shida kafin miƙa mulki*Dalilin da ya sa Buhari ke ta ɗaukar matakai – Fadar Shugaban Ƙasa *Ana shirin kawo cikas ga bukukuwan miƙa mulki a jihohi da ƙasa, inji DSS*Sa'o'i kafin miqa mulki Buhari ya umarci ministocinsa su cigaba da aikinsu*Ƙananan ministoci ba su da amfani a gwamnatin Buhari – Keyamo Daga MAHDI M. MUHAMMAD A ranar Litinin, 29 ga Mayu, 2023, gwamnatin sabon Shugaban Nijeriya mai jiran gado, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, za ta fara aiki a matsayin halastacciyar zaɓaɓɓiyar gwamnatin farar hula, yayin da…
Read More
Za a jinginar da filayen jirgin saman Kano da Abuja

Za a jinginar da filayen jirgin saman Kano da Abuja

*Za a ƙara ciwo bashin Dala miliyan 800*Za a nutsar da kuɗin a shirin rage raɗaɗin cire tallafin fetur Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnatin Nijeriya ta amince a jinginar da filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe da ke Abuja da kuma Malam Aminu Kano da ke Kano. Gwamnati ta amince da wannan mataki ne a taron majalisar koli da aka gudanar ranar Laraba a Abuja. Ministan Sufirin Jiragen Sama a Nijeriya, Hadi Sirika, ya shaida wa BBC cewa za a jinginar da filin jirgin Abuja na shekara 20, sannan na Kano na tsawon shekara 30. Sirika ya ce taron…
Read More
Majalisar Wakilai ta amince wa Buhari karɓar bashin N368bn daga Bankin Duniya

Majalisar Wakilai ta amince wa Buhari karɓar bashin N368bn daga Bankin Duniya

Majalisar Tarayya ta Ƙasa ta amince wa Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari da ya kinkimo bashin Naira biliyan 368.7 (Dala miliyan 800) daga Bankin Duniya. Mamba a Kwamitin Majalisar Wakilai kan Sha'anin Bashi da Tallafi, Abubakar Yunusa Ahmad, shi ne ya bayyana haka a wani shiri da Tashar Channels Television ta yi da shi a ranar Juma'a. Sai dan majalisar ya ce ba za a yi amfani da bashin ba a gwamnatin Buhari mai ƙarewa. Yana mai cewa, gwamnati mai jiran gado ce za ta sarrafa bashin don cimma manufar da ta sa aka ciyo shi. A cewarsa, game da Dala…
Read More
Tinubu ya gana da Kwankwaso a Faransa

Tinubu ya gana da Kwankwaso a Faransa

Daga BASHIR ISAH Zaɓaɓɓen Shugaban Ƙasa mai jiran gado, Bola Ahmed Tinubu, ya gana da ɗan takarar shugaban ƙasa na Jam'iyyar NNPP, Rabiu Kwankwaso, a Paris, babban birnin ƙasar Faransa. Bayanai sun ce Tinubu da Kwankwaso sun yi ganawar sirri bayan haɗuwar tasu inda suka shafe sa'o'i huɗu suna tattaunawa. Majiyarmu ta ce tattaunawar tasu ta shafi yadda za a yi tafiya tare da Kwankwaso a gwamnati mai jiran gado kasancewar Tinubu na da ra'ayin kafa gwamnati ta haɗin kan ƙasa. Kazalika, majiyar ta ce daga cikin batutuwan da suka tattauna har da batun shugabancin majalisar tarayya. Wadanda suka halarci…
Read More
ASUU ta caccaki Buhari kan sake cin bashi

ASUU ta caccaki Buhari kan sake cin bashi

*Buhari ya nemi majalisa ta ba shi damar ƙara ciwo bashi*Ya na son ciwo qarin bashin Naira biliyan 368.7 ne*Kwanaki 16 suka rage masa a gadon mulki Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Ƙungiyar Malaman Jami’o’i a Nijeriya (ASUU) ta bayyana buƙatar Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari na neman Majalisar Dattawa ta sahale masa ya ciwo bashin Naira Biliyan 368.7 a matsayin wani abin da bai dace ba kwanakin kaɗan kafin barin shi mulki. Farfesa Emmanuel Osodeke, Shugaban Ƙungiyar ASUU na Ƙasa, ya bayyana haka ne a jiya Alhamis yayin da yake jawabi a wajen bikin bayar da lambar yabo ta…
Read More
Majalisar Dokoki: A karon farko jam’iyyun adawa na shirin kafa shugabanci

Majalisar Dokoki: A karon farko jam’iyyun adawa na shirin kafa shugabanci

*Yadda fafatawar neman shugabancin Majalisar Dokokin Nijeriya yake ƙamari Daga MAHDI M. MUHAMMAD Makonni ƙalilan kafin a rantsar da Majalisar Dokokin Nijeriya ta 10, a karon farko jam’iyyun adawa a ƙasar su na ƙara samun ƙwarin gwiwar yin yunƙurin naɗa shugabanci a majalisar, musamman ma Majalisar Wakilai, wacce yawansu ya ɗari na jam’iyya mai mulki, wato APC. To, sai dai kuma ita ma APC ɗin tana cigaba da jan ɗamara kan sai ta ga abinda ya ture wa buzu naɗi. A karon farko dai a tarihin Nijeriya an zaɓi mambobin jam’iyyun adawa har sun fi na jam’iyya mai mulki bayan…
Read More
Almudahanar N2.1bn: Kotun Ɗaukaka Ƙara ta tabbatar da hukuncin da aka yanke wa Maina

Almudahanar N2.1bn: Kotun Ɗaukaka Ƙara ta tabbatar da hukuncin da aka yanke wa Maina

*Maina zai shafe shekara takwas a gidan kaso Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke Abuja ta tabbatar da hukuncin ɗaurin shekara takwas da aka yanke wa tsohon Shugaban Kwamitin Kula da Fansho, Abdulrasheed Maina kan yin sama-da-faɗi da kuɗaɗen fansho Naira biliyan 2.1. Alƙalan da suka saurari shari'ar, baki ɗaya su ukun sun yi ittifaƙi kan tabbatar da hukuncin da aka yanke wa Maina kamar yadda Mai Shari'a Okon Abang ya karanto. Jagoran alƙalan, Elfreda Williams-Daudu, ya tabbatar da hukuncin da Babbar Kotu ta yanke wa Maina ɗin wanda a kan haka shi Maina ya ɗaukaka ƙara. Alƙalin ya ce an…
Read More
‘Yan bindiga sun kashe mutum 40 a Kebbi da Zamfara

‘Yan bindiga sun kashe mutum 40 a Kebbi da Zamfara

Rahotanni daga jihohin Zamfara da Kebbi sun ce 'yan bindiga sun kashe aƙalla mutum 40 a ƙauyukan jihohin yayin harin da suka kai da asubahin ranar Lahadi. Jaridar Daily Trust ta rawaito cewar, wasu 'yan sanda guda shida na daga cikin mutum 36 da 'yan bindigar suka kashe a Ɗan Umaru da ke yankin Zuru a Jihar Kebbi. Mazauna yankin sun ce an yi jana'izar mutum 27, sannan wasu da dama sun jikkata sakamakon harin. Kazalika, sun ce 'yan bindigar sun sace mutane da dama haɗi da shanun jama'a yayin harin da suka kai ƙauyuka maƙwafta. Bayanai sun ce maharan…
Read More
Mun gyara aikin soja a Nijeriya – Shugaba Buhari

Mun gyara aikin soja a Nijeriya – Shugaba Buhari

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya bayyana cewa, an cimma ƙwararan shirin inganta tsaro a Nijeriya, tare da inganta kayan aiki, horar da jami’ai da tsarin jin daɗin jama’a da ya shafi fiye da yara 50,000 na jaruman sojojin da suka mutu. Da yake jawabi a Abuja ranar Alhamis, a wani bikin da ya samu halartar tsaffin shugabannin ƙasar biyu, shugaban ƙasa, Janar Yakubu Gowon da shugaban ƙasa, Goodluck Jonathan, shugaban ƙasar ya ce, ya kafa aikin ɗaukar sojoji 60,000 a aikin soja, kuma dubbai aka yaye daga makarantar horar da sojoji ta Nijeriya da sauran cibiyoyin…
Read More
An dakatar da cire tallafin fetur a Nijeriya

An dakatar da cire tallafin fetur a Nijeriya

Daga MAHDI M. MUHAMMAD A ƙarshe dai, Gwamnatin Tarayya ta yanke shawarar tsawaita wa’adin cire tallafin man fetur har bayan wa’adin Shugaba Muhammadu Buhari a karagar mulki. Ministar Kuɗi, Kasafi da Tsare-Tsaren Ƙasa, Zainab Ahmed ce ta bayyana hakan a wannan Alhamis yayin da ta ke zantawa da manema labarai a Abuja. A cewarta, Majalisar Tattalin Arziki ta Ƙasa NEC ce ta yanke shawarar cewa ba yanzu ne lokacin da ya dace a cire tallafin man fetur ba a ƙasar. Ministar wadda ta bayyana hakan bayan kammala zaman majalisar wanda Mataimakin Shugaban Ƙasa, Farfesa Yemi Osinbajo ya jagoranta, ta ce…
Read More