Ra’ayin Manhaja

Barkan mu da sallah!

Barkan mu da sallah!

Daga NASIR S. GWANGWAZO A cikin wannan satin, wato ranar Talatar da ta gabata, 20 ga Yuli, 2021, ne ɗaukacin al’ummar Musulmai da ke a faɗin duniya su ka gudanar da shagulgula na bikin Babbar Sallah, wato Sallar Layya, inda masu hali su ka yanka ragunansu na layya. Layyar an gudanar da ita ne a don tuna wa da Annabi Ibrahim (AS) a lokacin da Allah ya umarce shi ya yanka ɗansa, Annabi Isma’il (AS), a Dutsen Arafat, don bin umarnin da Allah ya ba shi. Don bin umarnin na Allah (SWT) Annabi Ibrahim (AS) da ɗan nasa, Annbai Isma’il (AS),…
Read More
Nijeriya na neman addu’ar kowa!

Nijeriya na neman addu’ar kowa!

Daga NASIR S. GWANGWAZO Mafi yawan talakawan Nijeriya sun yi tsammanin cewa, kawo yanzu ’yan ƙasar sun fita daga cikin halin ƙuncin da suka tsinci kansu a ƙarƙashin gwamnatocin baya, to amma har yanzu al’amura sun ƙi miƙewa, su tafi yadda ya kamata, duk da cewa, an zaɓo shugaban da ake da kyakkyawan zato a kansa, sannan kuma har kawo yanzu ba a taɓa zargin sa da aikata almundahana ko muna-muna da rashawa ba. To, amma duk da haka, baya ga tsananin halin talauci, fatara da ƙuncin rayuwa da talaka a Nijeriya ke fama da su, a yanzu dai kullum…
Read More
Shin da gaske ne Gwamnatin Buhari na zuba dukiya a harkokin tsaro?

Shin da gaske ne Gwamnatin Buhari na zuba dukiya a harkokin tsaro?

Daga NASIR S. GWANGWAZO A yanayin halin da Nijeriya ta tsinci kanta a ciki yanzu, ba kowa ne ya sani ko zai iya gane ƙoƙarin Gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari kan sha’anin tsaro ba, saboda yadda ake ci gaba da samun tangarɗa da cikas wajen shawo kan lamarin tsaro, wanda ya addabi al’umma, amma ko babu komai, za a iya cewa, haƙiƙanin ta’addanci da Boko Haram ta miƙe ƙafa ta na yi a gwamnatin baya, yanzu ya zama tarihi. A yanzu babu ƙaramar hukuma ko guda ɗaya a hannun Boko Haram, duk da cewa, gwamnatin baya ta sadar wa ƙungiyar ƙananan…
Read More
Sakamakon Jarrabawar JAMB da barazanar ilimi a Nijeriya

Sakamakon Jarrabawar JAMB da barazanar ilimi a Nijeriya

Daga NASIR S. GWANGWAZO a Abuja Kwanan nan ne Hukumar Kula da Shirya Jarrabawar Shiga Manyan makarantu a Nijeriya (JAMB) ta saki sakamakon jarrabawar ɗalibai na zangon 2020/2021, sakamakon da ya ja hankali kuma ya ɗaga hankali a faɗin ƙasar, saboda yadda ɗalibai suka faɗi warwas a jarrabawar. Sakamakon jarrabawar ya nuna cewa, a cikin ɗalibai 6,944,368 da suka zauna jarrabawar, guda 973,384 ne kacal suka tsallake shingen shiga jami’a. Hakan ya na nuni da cewa, kashi 14 cikin 100 ne kacal suka haye maki 180 da hukumar ta gindaya a matsayin shingen da ɗalibi zai haye, kafin ya samu…
Read More
Faruk Lawan: Ina aka kwana kan babban batun?

Faruk Lawan: Ina aka kwana kan babban batun?

A tsakiyar makon nan ne wata Babbar Kotu a Abuja ta yanke wa fitaccen tsohon ɗan Majalisar Wakilai na Tarayyar Nijeriya, Hon. Faruk Lawan, hukuncin ɗaurin shekaru bakwai a gidan yari bayan da ta ce kama shi da laifin amsar na goro daga hannun wani babban attajiri kuma ƙasurgumin ɗan kasuwa a ƙasar, wato Mista Femi Otedola a shekara ta 2012 lokacin da Lawan ]in ke shugabantar Kwamitin Bincike kan Badaƙalar Tallafin Man Fetur. A yayin da ta ke yanke hukuncin, alaƙalin kotun, Mai Shari’a Angela Otaluka, ta ce, Hon. Lawan ya kasa tabbatar wa da kotu iƙirarinsa na cewa,…
Read More
Ranar Dimukraɗiyya: Gwamnati na murna wasu na zanga-zanga

Ranar Dimukraɗiyya: Gwamnati na murna wasu na zanga-zanga

A ranar Asabar ɗin da ta gabata ne Nijeriya ta yi bikin cika shekara 22 da komawar ƙasar kan turbar dimokuraɗiyya, inda mahukunta da `yan ƙasa suke ƙididdigar nasarori da kuma tarin ƙalubalen da ƙasar ta fuskanta da kuma wanda take kan fuskanta. Wannan shi ne karon farko da ake bikin a wannan rana tun bayan sauya ranar bikin daga 29 ga watan Mayu zuwa 12 ga watan Yuni da hukumomin ƙasar suka yi a shekarar da ta gabata, don tunawa da zaɓen MKO Abiola; Zaɓen da aka gudanar a ranar 12 ga watan Yunin 1993 wanda a lokacin mutane…
Read More
Rikicin Tiwita: An bar jaki, ana dukan taiki

Rikicin Tiwita: An bar jaki, ana dukan taiki

A makon jiya ne, Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari ya aike da wanikakkausan saƙo ga waɗanda suka addabi ƙasarsa da fitinar tsaro ta hanyar kashe rayuka, ɓarnata dukiya da kai wa ofisoshin gwamnati hare-hare. Shugaban yana mayar da martani ni kai-tsaye kan ƙungiyar ’yan ta’addar nan ta IPOB mai fafutukar kafa Ƙasar Biyafra, wacce a kwanakin nan ta ke kai hare-haren ta’addanci kan ofisoshin hukumar INEC da na ’yan sanda a yankin Kudu maso Gabas. Shugaba Buhari ya kuma yi furucin ne a Fadar Shugaban Ƙasa lokacin da Shugaban Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, ya kai masa…
Read More
Murza gashin baki da Buhari ya yi

Murza gashin baki da Buhari ya yi

A yamma ranar 1 ga Yuni, 2021, Shugaban Ƙasar Nijeriya, Muhammadu Buhari, ya yi wani furuci ma jan hankalin da ya dace da buƙatar Nijeriya da ’yan Nijeriya, wanda kuma ba kasafai ake samun sa aikata irin waɗannan kalamai ba. A taƙaice ma dai, gwamnatinsa ba ta cika yin irinsu ko da da yawunsa ne tun bayan kafuwarta a watan Mayu na shekara ta 2015 zuwa yanzu a watan Yuni na shekara ta 2021. Da yawa suna alaƙanta hakan da kasancewar Shugaban Ƙasar dattijo, Hausa-Fulani, ɗan Arewa, gogagge da sauran ɗabi’u makamantan hakan, waɗanda su ne suke sanya ake kallon…
Read More
Hana kiwo a Kudu da raba kan Nijeriya

Hana kiwo a Kudu da raba kan Nijeriya

A makon nan ne Ƙungiyar Dattawan Arewacin Nijeriya (NEF) ta mayar wa ƙungiyar gwamnonin kudancin ƙasar nan da martanin cewa, su na gina mutanen da ke da tsananin nuna ƙabilanci da kuma ɓuya a bayan su suna tinzira jamaar su domin raba kan al'ummar ƙasa, wadda sanarwar hakan ke ɗauke da sa hannun Kakakin ƙungiyar, Dr. Hakeem Baba-Ahmed, da suka zargi gwamnonin da suka yi rantsuwar kare kundin tsarin mulki da taimaka wa masu fafutukar raba kan ƙasa da al'umma baki ɗaya. Ƙungiyar Dattawan Arewan ta bayyana matakin da gwamnonin kudancin ƙasar suka ɗauka na hana yawon kiwo a matsayin…
Read More
Buhari da ziyarar sa a ƙasar Faransa

Buhari da ziyarar sa a ƙasar Faransa

A kwanaki kaɗan da suka gabata, wato ranar 16 ga Mayu, 2021, ne, Shugaban Nijeriya, Muhammadu Buhari, ya buga bulaguro zuwa Birnin Paris, babban birnin Ƙasar Faransa, inda Shugaban ƙasar ta Faransa, Emmanuel Macron, ya karɓi baƙuncin shugabannin ƙasashen Afrika a taron tattaunawa kan jikkatar da aka sha sakamakon ɓarkewar annobar Cutar Korona da kuma duba yiwuwar samun tallafi, musamman bisa irin bashin da ya yi wa ƙasashen na Afrika katutu, sannan kuma ya ke ci gaba da ƙaruwa. Sai dai kuma, a sanarwar da Fadar Shugaban Nijeriya da ke Abuja ta bayar mai ɗauke da sa hannun Babban Mai…
Read More