Month: January 2021

Shugaban INEC ya buƙaci Majalisar Tarayya ta dage kan kwaskwarimar dokar zaɓe

Shugaban INEC ya buƙaci Majalisar Tarayya ta dage kan kwaskwarimar dokar zaɓe

Daga WAKILIN MU Shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, ya yi kira ga 'yan Majalisar Tarayya da su yi aiki ba tare da la'akari da jam'iyyar da kowanne ke wakilta ba wajen yi wa Dokar Zaɓe garambawul wanda zai taimaka wajen inganta yadda ake gudanar da zaɓe a ƙasar nan. Yakubu ya yi wannan kiran ne a wajen bikin ƙaddamar da kwamitin haɗin gwiwar ƙwararru na yi wa Dokar Zaɓe kwaskwarima wanda aka yi a Abuja a ranar Juma'a. Kwamitin Haɗin Gwiwar Majalisar Tarayya kan Hukumar Zaɓe da Al'amuran Zaɓe ne ya shirya taron tare da tallafin…
Read More
Shin ya dace a taya daliban Kankara murnar sace su?

Shin ya dace a taya daliban Kankara murnar sace su?

Tare da NASIRU ADAMU EL-HIKAYAWannan tambaya ce da ni marubuci na yi wa kai kuma na ke son ba da amsa da kai na. Da farko ma na so kai tsaye na radawa rubutun nan suna "Ina taya daliban Kankara murnar sace su!." Gaskiya zai iya yin ma'ana idan a ka ce sace 'yan makarantar nan da duk alamu ke nuna 'ya'yan talakawa ne ya jawo hankalin duniya ya koma kan su. Hatta mutan kudancin Najeriya sun ciccije sun koyi yanda a ke furta Kankara a jihar Katsina. Yanzu ka na shiga yanar gizo ka rubuta Kan...a injin bincike za…
Read More
Hanyoyin da gwamnati za ta inganta tattalin arziki da magance fatara – Shugaban Bankin Jaiz

Hanyoyin da gwamnati za ta inganta tattalin arziki da magance fatara – Shugaban Bankin Jaiz

Daga UMAR M. GOMBE ALHAJI HASSAN USMAN shi ne Babban Manajan Darakta na Bankin Musulunci na farko a Nijeriya, wato Bankin Jaiz. A wannan hirar da Mataimakin Editan Manhaja, UMAR MOHAMMED GOMBE ya yi da shi, qwararren masanin tattalin arzikin ya bayyana abubuwa da dama da suka hada da koma-bayan tattalin arziki da Nijeriya ke fuskanta da hanyoyin da za a magance su. Haka kuma ya yi tsokaci kan alfanun bayar da zakka da kuma gudunmawar da bankuna ke bayar wa ta fuskar inganta tattalin arziki, musamman bankunan Musulunci. MANHAJA: Ran ka ya dade, a matsayin ka na qwararre a…
Read More
Kalubalen da na fuskanta a aikin jarida – Madina Dauda Nadabo

Kalubalen da na fuskanta a aikin jarida – Madina Dauda Nadabo

Daga AYSHA ASAS HAJIYA MADINA DAUDA NADABO gogaggiyar ‘yar jarida ce wacce ta dade tana bayar da gagarumar gudummawa wajen dauko rahotanni da watsawa a sassan duniya, kuma qwararriyar ‘yar jarida wadda take nuna qwarewar aiki wajen gabatar da shirye-shirye masu ilimantarwa, nishadantarwa gami da zaburarwa. Manhajata yi hira da ita don jin gwagwarmayar ta a fannin aikin jarida kamar haka: Hajiya duk da ke ba boyayya ba ce wajen mutane, amma za mu so jin taqaitaccen tarihinki a taqaice. To, Assalamu alaikum. Da farko dai suna na Madina Dauda Nadabo. An haife ni a Unguwar Shanu da ke cikin…
Read More
Al’jabi: Damisar da ta kamu da Annobar Korona

Al’jabi: Damisar da ta kamu da Annobar Korona

Daga UMAR M. GOMBE An samu wata Damisar yankin qanqara mai kimanin shekara biyar da haihuwa mai suna NeeCee da cutar Korona Baros, bayan da aka yi ma ta gwajin qwayar cutar a farkon wannan makon. Gwajin wadda a matakin farko ya nuna cewa ta na dauke da qwayar SARS-CoV-2, wadda ke rikidewa zuwa COVID-19 ga bil’adama. Mujallar Courier-Journal ce ta ruwaito wannan abin al’ajabi da ya faru a wani gidan Zoo dake garin Louisville a Jihar Kentucky ta Qasar Amurka. A ranar Juma’ar nan ne hukumar gidan Zoo din ta sanar da hakan, ta na mai cewa an yi…
Read More
Ciyaman Nda-Isaiah: Ba rabo da gwani ba…

Ciyaman Nda-Isaiah: Ba rabo da gwani ba…

Daga IBRAHIM SHEME Tun a ranar farko da na fara haduwa da Mista Sam Nda-Isaiah, cikin mintuna kadan, ya dauke ni aiki. A lokacin ya na fafutikar neman wani qwararre wanda zai nada editan sabuwar jaridar sa mai suna LEADERSHIP, har wani tsohon dan jarida ya ba shi suna na. Rannan ya je Sakkwato domin nuna wa Gwamna Attahiru Bafarawa jaridar tasa, sai su ka hadu da wani aboki na a ofishin da su ke jira a yi wa kowannen su iso, domin ba tafiyar su daya ba, ba su ma san juna ba. Su na labari, sai abokin nawa…
Read More
Abota ita ce auren zamani

Abota ita ce auren zamani

Tare da AISHATU GIDADO IDRIS Zai iya yiwuwa ku kan yi wani tunani irin nawa, na cewar yawancin lokaci idan mutane ba su samu dama ko sa'ar auren wadanda su ke so ba, su kan samu aqalla wadanda su su ka fi alheri a gare su. Haka abin yake! Domin sau da yawa wasu su kan yi qorafin cewa rayuwa ta juya masu baya idan su ka rasa abin da su ka fi da so. Ba haka ba ne kuma. Tabbas, ana yawan auren soyayya, amma kuma ana yawan aure na sa'a, dace ko auren sakamako a kan rasa wani…
Read More
Kotu ta garqame asusun bankunan dan majalisa a Kaduna

Kotu ta garqame asusun bankunan dan majalisa a Kaduna

Daga ABBA MUHAMMAD, a KadunaBabar Kotun Jihar Kaduna ta ba da umurnin a garqame asusun ajiyar bankuna har guda 14 na dan majalisar jiha mai wakiltar Doka da Gabasawa a Majalisar Dokokin Jihar Kaduna, wanda shi ne shugaban masu rinjaye na majalisar, Honarabul Haruna Inuwa Dogo Mabo. Kotun ta bayyana cewa ta dauki wannan mataki ne a bisa samun sa da laifin cin amana da zamba cikin aminci da kuma sama da fadi da kunnen qashi da ya nuna wajen qin biyan dimbin basussuka na kudaden da ya amsa a hannun jama’a da sunan bashi.Wannan bayanin ya fito ne daga bakin…
Read More
Ba Allah ne ya jefa Nijeriya halin da ta shiga ba – Obasanjo

Ba Allah ne ya jefa Nijeriya halin da ta shiga ba – Obasanjo

Daga UMAR M. GOMBE, a Abuja A cin wani saqon da ya aike na shiga sabuwar shekara, Tsohon Shugaban Qasa, Olusegun Obasanjo, ya qalubalanci Shugaban Qasa, Muhammadu Buhari da sauran shugabanni da su daina dora alhakin halin da Nijeriya ke ciki kan Ubangiji, su zargi kansu kurum. Obasanjo ya bayyana haka ne a dakin karatun sa mai suna Olusegun Obasanjo Presidential Library dake Abeoluta a Jihar Ogun a wani saqonsa barka da sabuwar shekara da ya saba aikewa a duk qarshen shekara. Tsohon shugaban qasan ya nuna qin amincewar sa cewa, Allah ne Ya qaddara halin talauci da Nijeriya ke…
Read More
Shugaban Majalisar Dattawa ya taya ‘yan Nijeriya murnar sabuwar shekara

Shugaban Majalisar Dattawa ya taya ‘yan Nijeriya murnar sabuwar shekara

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Ahmed Lawan ya taya dukkan ’yan Nijeriya murnan shiga sabuwar shekarar 2021. Yana mai cewa Shekarar 2020 ta zo ma daukacin kasashen duniya cike da kalubale na tattalin arziki, tsaro, lafiya da sauran fannunuka. “Amma Alhamdulillah duk da haka, wadannan kalubalen ba su karya mana gwiwa na ganin samun kyakykyawar makoma a matsayin mu na mutane da kuma kasa ba. A matsayin mu na majalisar dokoki, mun dade da tsara yadda zamu tunkari abubuwan da shekarar 2020 ta zo da su ta hanyar yin dokokin da za su tabbatar da gudanar da kyakykyawan mulki da cigaban…
Read More