Month: April 2021

Sanata Ordia ya tsallake rijiya da baya sau biyu a yini guda

Sanata Ordia ya tsallake rijiya da baya sau biyu a yini guda

Daga FATUHU MUSTAPHA Har sau biyu 'yan bindiga na kai wa Sanata Clifford Ordia (PDP Edo ta Tsakiya) hari a Litinin da ta gabata a hanyar Okenne zuwa Lokoja da kuma hanyar Lokoja zuwa Abaji. Sanata Ordia wanda shi ne shugaban kwamitin Majalisar Dattawa kan Basussukan Cikin Gida da Waje, ya yi wa manema labarai bayanin yadda ya kuɓuta daga harin 'yan bindigar da suka buɗe wa tawagar motocinsa wuta a kan hanyarsa ta komawa Abuja daga jihar Edo. Ya ce sakamakon musayar wuta da aka yi tsakanin jami'an tsaron da ke ba shi kariya da ɓarayin, wasu 'yan sanda…
Read More
Majalisa ta yi kumfar baki kan yadda tsaron Nijeriya ya dagule

Majalisa ta yi kumfar baki kan yadda tsaron Nijeriya ya dagule

Daga UMAR M. GOMBE Majalisar Dattawan Nijeriya ta bayyana cewa taɓarɓarewar tsaron ƙasa abin kunya ne ga Nijeriya. Majalisar ta bayyana haka ne a zamanta na Talatar da ta gabata, inda sanatoci da dama suka nuna takaicinsu kan mummunan halin da tsaron ƙasa ya faɗa. Sa'ilin da yake tofa albarkacin bakinsa a muhawarar da aka tafka a zauren Majalisar, Sanata Birma Enagi (APC Neja ta Kudu) ya ce, "Tabbas lamari ya lalace kuma abin kunya ne. Gwamnatin Tarayya ta yi sakwa-sakwa wajen yaƙi da ɓarayin daji da 'yan Boko Haram." Ya ce, "Mafi takaicin abin da ke faruwa shi ne…
Read More
Kwastam ta kama kwantena maƙare da miyagun ƙwayoyi a Legas

Kwastam ta kama kwantena maƙare da miyagun ƙwayoyi a Legas

Daga WAKILINMU Hukumar Yaƙi da Fasa-ƙwauri ta Ƙasa da ke yankin Apapa a jihar Legas, ta ce ta kama wani sunduƙin safarar kayayyaki maƙare da ƙwayoyin taramol da kodin waɗanda masu tu'ammali da miyagun ƙwayoyi kan yi amfani da su don shiga yanayi na maye. Bayanan hukumar sun nuna a Litinin da ta gabata jam'ian hukumar suka kama sunduƙin a Legas mai ɗauke da katan-katan na ƙwayar taramol guda 124 da na kodin guda 805. Rahotanni sun ce masu fasa-ƙwaurin sun yi ɓad da sawu ta hanyar ɗora tukwane a kan ƙwayoyin da nufin kada jami'an kwastam su gano shirinsu.…
Read More
NUJ ta yi kira ga NBC da ta janye tarar milyan 5 da ta ɗora wa tashar Channels

NUJ ta yi kira ga NBC da ta janye tarar milyan 5 da ta ɗora wa tashar Channels

Daga AISHA ASAS Ƙungiyar 'Yan Jarida ta Ƙasa (NUJ) ta yi kira ga Hukumar Kula da Kafafen Yaɗa Labarai ta Ƙasa (NBC) da ta tsananta lura game da yadda take ɗaukar mataki a kan kafafen yaɗa labarai a cikin ƙasa. Shugaban ƙungiyar na ƙasa, Chris Isiguzo, ya ce sun yi mutuƙar damuwa da barazanar da hukumar NBC ta yi na dakatar da lasisin tashar talabijin ta Channels saboda tattaunawar da ta yi da mai magana da yawun tsegerun IPOB a wani shirinta da tashar ta gabatar kwanan nan. NUJ ta ce tana buƙatar NBC ta gaggauta janye tarar milyan N5…
Read More
Nijeriya za ta karɓi rigakafin korona samfurin Johnson & Johnson guda milyan 29.8

Nijeriya za ta karɓi rigakafin korona samfurin Johnson & Johnson guda milyan 29.8

Daga WAKILINMU Gwamnatin Nijeriya na sa ran ta karɓi allurar rigakafin cutar korona samfurin Johnson & Johnson (J&J) ƙwara milyan 29.8, kamar yadda Dr Faisal Shuaib ya bayyana a Litinin da ta gabata. Shuaib wanda shi ne Daraktan Hukumar Bunƙasa Lafiya a Matakin Farko ta Ƙasa (NPHCDA), ya bayyana haka ne yayin taron manema labarai na mako-mako da aka saba gudanarwa game da sha'anin yaƙi da cutar korona a Abuja. Ya ce gwamnati ta sanya hannun karɓar rigakafin ne ta Ƙungiyar Ƙasashen Afirka (AU), sannan maganin zai shiga hannu ta shirin COVAX ya zuwa ƙarshen Mayu ko farkon Yuni. Jami'in…
Read More
Boko Haram sun karɓe Kaure har sun kafa tutarsu – Gwamna Bello

Boko Haram sun karɓe Kaure har sun kafa tutarsu – Gwamna Bello

Daga AISHA ASAS Gwamna Abubakar Sani Bello na jihar Neja ya tabbatar da 'yan Boko Haram sun shigo jihar Neja musamman ma a yankin Kaure da ƙaramar hukumar Shiroro, kuma har ma sun kafa tutarsu. Gwamna Bello ya sanar da hakan ne sa'ilin da ya ziyarci 'yan gudun hijira su sama da 3000 daga yankin ƙaramar hukumar Shiroro da Munya da suka yi sansani a harabar makarantar Firamare ta Ibrahim Badamasi Babangida (IBB) da ke Minna. A cewarsa, "Ina mai tabbatar da cewa akwai ɓurɓushin Boko Haram a Neja, a yankin Kaure. "Na samu bayanin har sun kafa tutarsu a…
Read More
‘Yan bindiga sun raba ƙauyuka 50 da matsugunansu a Neja – Gwamna Bello

‘Yan bindiga sun raba ƙauyuka 50 da matsugunansu a Neja – Gwamna Bello

Daga BASHIR ISAH Gwamnan jihar Neja, Alhaji Abubakar Sani Bello, ya ce aƙalla ƙauyuka 50 ne 'yan bindiga suka raba da mazauninsu a tsakanin ƙananan hukumomi biyar a jihar, lamarin da a cewar gwamnan ya haifar da rikicin jinƙai a jihar. Gwamna Bello ya bayyana haka ne a lokacin da yake buɗe taron bita na yini biyu kan inganta hanyayoyin tara kuɗaɗen shiga ga ƙananan hukumomi, a garin Minna babban birnin jihar. Gwamnan ya ce akwai buƙatar shirya wannan taro, tare da jaddada buƙatar da ke akwai ƙananan hukumomin jihar su matse ƙaimi wajen tara wa gwamnatin kuɗaden shiga ta…
Read More
NBC ta dakatar da tashar Channels saboda tattaunawa da jagoran IPOB

NBC ta dakatar da tashar Channels saboda tattaunawa da jagoran IPOB

Hukumar Kula da Gidajen Rediyo da Talabijin ta Ƙasa (NBC), ta dakatar da gidan talabijin na Channels har da ƙarin tarar milyan N5 sabida take dokar aiki. A wata wasiƙa da ta aike wa Manejin Daraktan tashar wadda ta sami sa hannun Muƙaddashin Babban Daraktan Hukumar, Prof. Armstrong Idachaba, NBC ta nuna ta ɗaiki wannan mataki ne ta kafa hujja da wani shirin kai-tsaye da tashar ta gabatar a ranar Lahadi, 25, Afrilu, 2021 da misalin ƙarfe bakwai na dare, inda ta kama tashar da laifin bai wa jagoran tsegerun IPOB damar faɗin maganganun da ka iya haddasa fitina ba…
Read More
Zulum ya naɗa Indimi da wasu matsayin majalisar gudanarwa ta jami’ar Barno

Zulum ya naɗa Indimi da wasu matsayin majalisar gudanarwa ta jami’ar Barno

Daga UMAR M. GOMBE Gwamnan jihar Barno, Babagana Umara Zulum, ya naɗa Majalisar Gudanarwa da za ta sanya ido kan gudanar da harkokin Jami'ar Jihar Barno. Zulum ya naɗa majalisar ne a ranar Litinin a fadar gwamnatin jihar, wadda za ta gudana ƙarƙashin jagorancin Alhaji Mohammed Indimi. Sauran mambobin majalisar sun haɗa da Farfesa Abubakar Mustapha, Farfesa Bankole Ogumbameru, Farfesa Shettima Umara Bulakarima, Alhaji Lawan Buba, wakilin majalisar dattawa na jami'ar da dai sauransu, yayin da rajistaran jami'ar zai kasance riƙe da muƙamin sakataren majalisar. Gwamnan ya yi kira ga 'yan majalisar da su samar da tsari mai inganci wajen…
Read More