Month: May 2021

Za a iya sace kowa a Arewa?

Za a iya sace kowa a Arewa?

Daga NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Ba mamaki a iya sace kowa musamman in dai mutum na yawo a sassan arewacin Nijeriya da dare ne ko ma da rana tsaka. Wannan lamari na satar mutane don neman kuɗin fansa ta zama babbar masana'antar samun kuɗaɗe ga miyagun irin daji dama watakila wasu a cikin gari. Wata dabara ma da matafiya tsakanin Abuja da Kaduna ke yi ita ce bin jirgin ƙasa don kauce wa gamuwa da ɓarayin a titi a yankin nan na Rijana. Wannan dabarar ma akwai lokacin da ba ta ɓullewa don akwai labarin an sace mutane bayan sun sauka…
Read More
‘Yancin Zaɓi

‘Yancin Zaɓi

Daga AMINA HASSAN ABDULSALAM Kwanaki na haɗu da wata uwa wace ɗanta ya sami gurbin karatun injiniya a jami’a, bayan ya biya kuɗin na gani na karɓa, wato acceptance fee sai aka ce masa ai ya yi kuskuren haɗin gambiza a jarabawar samin gurbin karatun jami’a wato jamb ko UME ɗin sa don haka an janye gurbin karatu da aka ba shi. Iyayen yaron ganin yadda yake da ƙwazo suka yi duk yadda za su yi yaron ya karanta abinda ransa ke muradi abin ya faskara, a ƙarshen sai wani kwas ɗin aka ba shi wanda bai kai na injiyan…
Read More
Adawa da siyasantar da matsalar tsaro ba za ta fisshe mu ba

Adawa da siyasantar da matsalar tsaro ba za ta fisshe mu ba

A wannan yanayi da mu ke ciki yanzu na taɓarɓarewar tsaro a sassab Nijeriya, jam'iyyun adawa, ƙungiyoyi masu zaman kansu da 'yan ba-ni-na-iya da kuma masu sharhi akan al'amuran yau da kullum a Nijeriya sun taso gwamnati gaba wajen sukar lamirin ta dangane da abinda ya shafi tsaron ƙasar. Yayin da wasu suke kalaman tunzurawa da ɓatanci tare da nuna siyasa ƙarara a cikin kalaman waɗansu. Wanda hakan yake ƙara rura wutar ƙiyayya tsakanin talaka da masu mulkin, talakawa ba sa ganin ƙoƙarin da gwamnati ke yi, har ta kai ga wasu na tunanin yi mata bore. Wasu kuwa suna…
Read More
Mafita: Me ya sa soyayya take mutuwa bayan aure?

Mafita: Me ya sa soyayya take mutuwa bayan aure?

Daga AMINA YUSUF ALI A makon da ya gabata ne muka zo muku da bayani a wannan jaridar taku ta Manhaja mai farin jini a game da dalilan da suke sanyawa soyayya ta mutu murus bayan aure. A waccan fitowar mun zano dalilai da yawa da sukan sa hakan ta faru. Wannan ya sa wasu makaranta da dama suka yi ta tururuwar kiran waya inda suke ƙorafin cewa an kawo musu cuta amma ba a samar musu da waraka ba. Shi ne ni kuma na yi linƙaya a kogin zamantakewa na tsamo muku wasu daga cikin hanyoyin da za su…
Read More
Taya murna ga gwarzon mawallafi: Mohammed Idris ya cika shekara 55, Blueprint ta cika 10

Taya murna ga gwarzon mawallafi: Mohammed Idris ya cika shekara 55, Blueprint ta cika 10

Daga IBRAHIM SHEME A rayuwa ta, akwai wasu mutum uku da nake kira ‘Chairman’, kuma dukkan su na da alaƙa fiye da guda da junan su. Da farko, su ukun nan daga Jihar Neja suka fito. Biyu daga cikin su ƙabilar Nupe ne, wato dai “Bayin Katsina” kenan. Amma batu na gaskiya, su ukun iyaye na ne. Ko me ya sa haka? Saboda sun taɓa ba ni aiki ko makamancin haka, wannan shi ne abu na biyu. Sai na uku, mutum biyu daka cikin su kowanne na ɗauke da muƙamin Kakakin Nupe, wanda Mai Martaba Etsu Nupe, Alhaji Yahaya Abubakar…
Read More
Gumi da Obasanjo sun taimaka wajen kuɓutar da daliban Kaduna 27 da aka yi garkuwa da su

Gumi da Obasanjo sun taimaka wajen kuɓutar da daliban Kaduna 27 da aka yi garkuwa da su

Daga WAKILINMU Bayanai daga jihar Kaduna, sun nuna an sako ɗaliban College of Forestry Mechanisation da ke Afaka a jihar su 27 da aka yi garkuwa da su. Ɗaya daga cikin waɗanda suka karɓi ɗaliban ne ya labarta wa jaridar Daily Trust batun. Majiyar Daily Trust ta ce kwamitin sulhu na Sheikh Ahmed Gumi shi ne ya shige gaba wajen kuɓutar da ɗaliban, tare da taimakon Tsohon Shugaban Ƙasa, Olusegun Obasanjo. Ɗaliban na daga cikin ɗalibai 37 da aka sace a jihar kusan watanni biyu da suka gabata. Inda bayan biyan kuɗin fansa da iyayen ɗaliban suka yi, sai 'yan…
Read More
Majalisar Dattawa za ta gana da hafsoshin tsaro kan sha’anin tsaron ƙasa

Majalisar Dattawa za ta gana da hafsoshin tsaro kan sha’anin tsaron ƙasa

Daga AISHA ASAS A ranar Alhamis ake sa ran Majalisar Dattawa ta karɓi baƙuncin manyan hafsoshin tsaron ƙasa da sauran hukumomin tsaro inda za a tattauna kan batun da ya shafi matsalolin tsaron ƙasa. Manhaja ta fahimci cewa buƙatar gayyatar jami'an ta taso ne duba da yadda sha'anin tsaron ƙasa ke ƙara daburcewa. Tun farko, Majalisar ta so ganawa da Shugaban Rundunar Sojoji da Babban Sufeton 'Yan Sanda da kuma Shugaban Hukumar Tattara Bayanan Sirri (NIA), a Talatar da ta gabata amma sai hakan bai yiwu ba sakamakon taron majalisar tsaro ta ƙasa ta gudanar. A bisa wannan dalili ne…
Read More
Ganduje ya yi wa Kano da Nijeriya fatan samun zaman lafiya mai ɗorewa

Ganduje ya yi wa Kano da Nijeriya fatan samun zaman lafiya mai ɗorewa

Daga WAKILINMU Gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya yi addu'ar Allah Ya bai wa jiharsa Kano da ma Nijeriya baki ɗaya dauwamammen zaman lafiya. Ganduje ya gabatar da wannan addu'a ne a ranar Laraba sa'ilin da yake gudanar da Umura tare da iyalansa a Saudiyya. Mai taimaka wa gwamnan kan sha'anin kafafen sadarwa na zamani, Abubakar Aminu Ibrahim, ya ce Ganduje ya yi Umurar ne tare da mai ɗakinsa Farfesa Hafsat Abdullahi Umar Ganduje, da ɗansa Engr. Umar Abdullahi Ganduje, da 'yarsa Dr. Amina Abdullahi Umar Ganduje, sai kuma mai taimaka masa kan harkokin cikin gida, Ahmad Abbas Ladan.…
Read More
Gwamnati ta soma nazarin rage albashin ma’aikata don rage kashe kuɗaɗe

Gwamnati ta soma nazarin rage albashin ma’aikata don rage kashe kuɗaɗe

Daga FATUHU MUSTAPHA Ga dukkan alamu, mai yiwuwa Gwamnatin Tarayya ta ɗauki matakin zabtare albashin ma'aikatanta a matsayin wani ɓangare na ƙoƙarin da take wajen ganin an rage yawan kuɗaɗen da ake kashewa wajen gudanar da harkokin gwamnati. Bayanan Ministar Kuɗi, Zainab Ahmed ne suka nuna haka a Talatar da ta gabata inda ta faɗa cewa lallai, gwamnati na ƙoƙarin duba yiwuwar rage kashe kuɗaɗen da take yi wajen harkokin gudanarwa. Ta yi wannan bayani ne a wajen taron tattauna batun rashawa da tsadar gudanar da gwamnati a Nijeriya wanda Hukumar Yaƙi da Rashawa da Laifuka Masu Alaƙa da Rashawa…
Read More
Malamai sun tsunduma yajin aiki a Neja

Malamai sun tsunduma yajin aiki a Neja

Daga UMAR M. GOMBE Malaman makarantun gwamnati a jihar Neja sun tsunduma yajin aikin sai baba ta gani a wannan Laraba. Cikin wata takardar sanarwa wadda Ƙungiyar Malamai ta Ƙasa (NUT) reshen jihar ta fitar cikin daren da ya gabata, NUT ta ce malaman firamare da na sakandare na gwamnati a jihar, sun soma yajin aikin ne saboda gazawa da gwamnatin jihar ta yi wajen biya wa malamai buƙatunsu kamar yadda aka yi yarjejeniya a baya. NUT ta ce kafin kai wa ga ɗaukar wannan mataki sai da ta tattauna da Shugaban Ma'aikata na jihar da manyan sakatarori a ranar…
Read More